ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Tuhumar Ƙananan Yara Da Laifin Shirya Juyin Mulki

by Ra'ayinmu
1 year ago
Yara

A kwanakin baya ne, kafafen yada labarai na cikin  gida da na kasashen waje suka kasance cike da labaran gurfanar da kananan yara da babbar kotun tarayya ta yanke masu hukuncin cin manar kasa saboda gudanar da zanga-zangar kawo karshen rashin gudanar da shugabanci na gari a Nijeriya da kuma sauran aikata laifuka.

Wani babban abin takaici shi ne, yadda kafafen yada labarai na kasashen waje suka wallafa cewar, gwamnatin kasar nan, za ta yankewa su yaran 29 hukuncin kisa saboda gudanar da halin yunwar da aka shiga a kasa.

  • Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Biyan Bashin Waɗanda Aka Tsare A Gidan Gyaran Hali

Sai dai kuma, wasu kwararrun Lauyioyi da kungiyoyin kare rajin ‘yancin ‘yan Adam a kasar, sun fito karara sun yi tir da kama yaran da mahukuntar kasar suka yi kan gudanar da zanga-zangar, musamman ma idan aka yi la’akari da yadda wasu daga cikin yaran da aka gurfanar a gaban babbar kotun tarayya bayan an gurfanar da su a gaban kotun domin bukatar bayar da belinsu.

ADVERTISEMENT

Kazalika ma, lamarin ya kuma kara yamutsewa hakan ya biyo bayan zargin da aka yi na cewa, a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan sanda, sun ci zarafin su, wadanda kuma ‘yan sandan suka mayar da su tamkar wadanda suka aikata wani babban laifi.

Makomar wadannan yaran dai, tasa tunawa da zanga-zangar #EndSARS wadda wasu jami’an tsaro suka yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin masu zanga-zangar a lokacin da suke kan yin zanga-zangar.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

Me yiyuwa sukar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sha ne, ya tilasata shi bayar da umarni nan take, da a saki yaran a kuma gaggauta mika su ga iyayensu.

A nan, muna jinjinawa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan ceto rayuwar yaran daga hannun jami’an tsaron, musamman ma  idan aka yi la’akari da irin wahalar da suka sha a hannun ‘yansanda.

A bisa tunanin, tun da farko bai kamata ma ace ‘yan sandan sun kama yaran ba, domin yaran dai, sun yi zanga-zangar ce kan kuncin rayuwa.

Zaman da yaran suka yi a kulle, hakan ya nuna cewa, an barsu ne a cikin yunwa da kasancewa a cikin rashin lafiya don kawai sun gudanar da zanga-zangar fargar da gwamnati kan ci gaba da kasancewar talakawan kasar, a cikin kangin talauci.

Kwanci tashi, irin juyin juya hali da ya auku a kasar Faransa, ya janyo kifar da masarautar garjiya ta kasar, musamman ma, ba wai don samun yawan talauci ba, amma saboda irin mulkin gurguzu da masarautar ke yiwa ‘yan kasar.

Kazalika ma, kasar Rasha ba wai an kifar da gwamnatin kasar ne da makamin kari dangi ne ba, abin ya kawo karshen shugabannin  kasar ba, amma boren da ‘yan kasar suka gudanar ne, ya kawo karshen shugabancin mahukuntar kasar, ya biyo bayan jefa rayuwarsu a cikin kangin rikcewar rayuwa.

Namu ra’ayin a nan shi ne, akasarin kasashe ba su koyon darasi a kan kuskuren da wasu kasashen suke tabkawa.

Abinda ke faruwa a Nijeriya shi ne, kusan matakan da bangaren gwamnatoci uku na kasar ke yi, ba su daukar kwararan matakan da suka dace.

Duk kasar da ta kasance kayan abinci da sauran kayan amfanin yau da kullum sun fi karfin talakan kasar, amma masu rike da madabun iko na siyasa, suna yin wandaka da watanda da kudaden gwamnati yadda suke so, suna kuma barin ‘ya’yan talakawa a cikin kangin halin yunwa, wannan babban abin bakin ciki ne.

Ra’ayinmu a nan irin yadda yaran suka tsinci kansu a cikin cin zarafin gwamnatin su, wadda ya kamata ta nuna cewa, mulkin dimokiradiyya ne ake gudanarwa a kasar hakan kuma ya nuna cewa, tamkar ana gudanar da mulkin mallakar Fir’aunanci ne a kasar.

A matsayin a wannan jaridar, mun nuna taikaicin mu a kan irin halin da yaran suka tsinci kansu a lokacin da aka tsare su, wanda kuma jami’an tsaro suka dauke su tamkar wasu masu mugun hadari a cikin alumma.

A bisa tunanin mu, irin wannan halin da aka jefa yaran a ciki, hakan zai iya juya tunanin su zuwa rungumar munanan dabi’u.

Ya zama wajbi mu ankarar da mahukunta don su gane cewa, ya kamata su san yadda za su rinka tafiyar da yara a duk lokacin gudanar da wata zanga-zanga, kamar dai irin ta #EndBadGobernance.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mutane 7 Ne Suka Rasu Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro Da Taifod Ba Wata Sabuwar Cuta Ba – Gwamnatin Kano
Ra'ayinmu

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

November 28, 2025
Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya
Ra'ayinmu

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

November 21, 2025
Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Next Post
Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima…

Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima...

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.