• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Tuhumar Ƙananan Yara Da Laifin Shirya Juyin Mulki

by Ra'ayinmu
9 months ago
in Ra'ayinmu
0
Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne, kafafen yada labarai na cikin  gida da na kasashen waje suka kasance cike da labaran gurfanar da kananan yara da babbar kotun tarayya ta yanke masu hukuncin cin manar kasa saboda gudanar da zanga-zangar kawo karshen rashin gudanar da shugabanci na gari a Nijeriya da kuma sauran aikata laifuka.

Wani babban abin takaici shi ne, yadda kafafen yada labarai na kasashen waje suka wallafa cewar, gwamnatin kasar nan, za ta yankewa su yaran 29 hukuncin kisa saboda gudanar da halin yunwar da aka shiga a kasa.

  • Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Biyan Bashin Waɗanda Aka Tsare A Gidan Gyaran Hali

Sai dai kuma, wasu kwararrun Lauyioyi da kungiyoyin kare rajin ‘yancin ‘yan Adam a kasar, sun fito karara sun yi tir da kama yaran da mahukuntar kasar suka yi kan gudanar da zanga-zangar, musamman ma idan aka yi la’akari da yadda wasu daga cikin yaran da aka gurfanar a gaban babbar kotun tarayya bayan an gurfanar da su a gaban kotun domin bukatar bayar da belinsu.

Kazalika ma, lamarin ya kuma kara yamutsewa hakan ya biyo bayan zargin da aka yi na cewa, a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan sanda, sun ci zarafin su, wadanda kuma ‘yan sandan suka mayar da su tamkar wadanda suka aikata wani babban laifi.

Makomar wadannan yaran dai, tasa tunawa da zanga-zangar #EndSARS wadda wasu jami’an tsaro suka yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin masu zanga-zangar a lokacin da suke kan yin zanga-zangar.

Labarai Masu Nasaba

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

Me yiyuwa sukar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sha ne, ya tilasata shi bayar da umarni nan take, da a saki yaran a kuma gaggauta mika su ga iyayensu.

A nan, muna jinjinawa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan ceto rayuwar yaran daga hannun jami’an tsaron, musamman ma  idan aka yi la’akari da irin wahalar da suka sha a hannun ‘yansanda.

A bisa tunanin, tun da farko bai kamata ma ace ‘yan sandan sun kama yaran ba, domin yaran dai, sun yi zanga-zangar ce kan kuncin rayuwa.

Zaman da yaran suka yi a kulle, hakan ya nuna cewa, an barsu ne a cikin yunwa da kasancewa a cikin rashin lafiya don kawai sun gudanar da zanga-zangar fargar da gwamnati kan ci gaba da kasancewar talakawan kasar, a cikin kangin talauci.

Kwanci tashi, irin juyin juya hali da ya auku a kasar Faransa, ya janyo kifar da masarautar garjiya ta kasar, musamman ma, ba wai don samun yawan talauci ba, amma saboda irin mulkin gurguzu da masarautar ke yiwa ‘yan kasar.

Kazalika ma, kasar Rasha ba wai an kifar da gwamnatin kasar ne da makamin kari dangi ne ba, abin ya kawo karshen shugabannin  kasar ba, amma boren da ‘yan kasar suka gudanar ne, ya kawo karshen shugabancin mahukuntar kasar, ya biyo bayan jefa rayuwarsu a cikin kangin rikcewar rayuwa.

Namu ra’ayin a nan shi ne, akasarin kasashe ba su koyon darasi a kan kuskuren da wasu kasashen suke tabkawa.

Abinda ke faruwa a Nijeriya shi ne, kusan matakan da bangaren gwamnatoci uku na kasar ke yi, ba su daukar kwararan matakan da suka dace.

Duk kasar da ta kasance kayan abinci da sauran kayan amfanin yau da kullum sun fi karfin talakan kasar, amma masu rike da madabun iko na siyasa, suna yin wandaka da watanda da kudaden gwamnati yadda suke so, suna kuma barin ‘ya’yan talakawa a cikin kangin halin yunwa, wannan babban abin bakin ciki ne.

Ra’ayinmu a nan irin yadda yaran suka tsinci kansu a cikin cin zarafin gwamnatin su, wadda ya kamata ta nuna cewa, mulkin dimokiradiyya ne ake gudanarwa a kasar hakan kuma ya nuna cewa, tamkar ana gudanar da mulkin mallakar Fir’aunanci ne a kasar.

A matsayin a wannan jaridar, mun nuna taikaicin mu a kan irin halin da yaran suka tsinci kansu a lokacin da aka tsare su, wanda kuma jami’an tsaro suka dauke su tamkar wasu masu mugun hadari a cikin alumma.

A bisa tunanin mu, irin wannan halin da aka jefa yaran a ciki, hakan zai iya juya tunanin su zuwa rungumar munanan dabi’u.

Ya zama wajbi mu ankarar da mahukunta don su gane cewa, ya kamata su san yadda za su rinka tafiyar da yara a duk lokacin gudanar da wata zanga-zanga, kamar dai irin ta #EndBadGobernance.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #EndBadGovernance
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alakar Sin Da Brazil Za Ta Samu Sakamako Mai Kyau A Shekaru 50 Masu Zuwa

Next Post

Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima…

Related

Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

4 weeks ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Ra'ayinmu

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

1 month ago
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
Ra'ayinmu

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

2 months ago
Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
Ra'ayinmu

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

2 months ago
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara
Ra'ayinmu

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

3 months ago
Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

4 months ago
Next Post
Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima…

Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima...

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.