ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima…

by Bello Hamza and Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Haraji

Watanni biyu da suka gabata, Shugaba Tinubu ya aike wa da majalisun kasar nan wani kudurin doka da yake neman sahalewarsu, kan wasu kundurori kamar haka;

-Kudurin Dokar Haraji ta Nijeiya ta 2024. -Kudurin Dokar Kula da Haraji – da Kudurin Dokar Samar da Hukumar Haraji ta Kasa (NRS) da kuma Kudurin Dokar Tattara Haraji ta Hadin Gwiwa.

  • Sin Ta Zargi EU Da Bayar Da Kariyar Cinikayya Bayan Da Kungiyar Ta Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin
  • Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

Sai dai wadannan kudurin dokokin sun gamu da cikas inda kungiyar gwamnonin Arewa sun soki lamarin kundurorin a yayin wani taro da suka yi a Kaduna a watan da ya gabata, musamman na harajin BAT wanda suka ce ya ci karo da wasu muradun Arewa. Wannan ta sa gwamnonin ba wa ‘yan majalisun jihohinsu umarnin yin watsi da wannan kuduri.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin kudurin dai ya kunshi sauya fasalin harajin BAT ta hanyar rage abin da gwamnatin tarayya ke samu daga kaso 15 zuwa 10.

A gefe guda kuma, kudurin ya kunshi bayanan tsarin yadda za a kasafta harajin da ake samu a kowacce jiha.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Haka kuma majalisar zartarwa ta tatalin arziki, wacce ta kunshi gwamnonin da mataimakin shugaban kasa, ta bukaci shugaban kasa ya janye wannan kudurin daga gaban majalisun kasar nan.

Sai dai shugaban kasa ya yi kunnen uwar shegu da bukatar tasu inda ya ce a bar majalisa ta yanke hukunci.

Jan hankalin da gwamnatin tarayya ta yi kan tsarin

A ci gaba da ganin koma bayan da wasu sassan kasar nan musamman ‘yan siyasar Arewa ke ke yi, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, batun tsarin gyaran harajin da ake yi, an tsara shi ne domin tallafa wa ci gaban da ake fuskanta, ta hanyar magance kalubalen da suka hada da yawaitar haraji, da wasu bukatu, da kuma rage nauyin haraji kan daidaikun mutane da kasuwanci.

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, maimakon nuna fargabar rashin gaskiya da masu adawa da tsarin garambawul din suka haifar, ya kamata ‘yan Nijeriya su fahimci cewa manufar ita ce inganta saukin kasuwanci, da saukaka ci gaban tattalin arziki mai dorewa, gami da wadata a’umma.

An samu cece-kuce cewa tsarin da aka gabatar na iya haifar da karancin kudaden shiga ga wasu jihohi, lamarin da zai iya ta’azzara talauci a Arewa.

A wani bayani da ya yi wa jaridar LEADERSHIP, Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa Kan Manufofin Kasafin Kudi da Sake Fasalin Haraji, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa sake fasalin ba zai yi illa ga wani bangare na kasar nan ba.

Ya yi nuni da cewa, kashi 5 da gwamnatin tarayya za ta bayar za a iya kebewa domin daidaita kudi saboda a magance duk wata gazawa ga jiha bisa sabon tsarin.

“Wannan yana tabbatar da cewa babu wata jiha da ta fi muni a cikin gajeren lokaci tare da inganta ayyukan tattalin arziki da kuma kudaden shiga ga dukkanin jihohi a cikin tsaka-tsakin lokaci zuwa dogon lokaci,” in ji Mista Oyedele.

Muhimman makasudan sake fasalin harajin sun hada da adadin haraji mai lamba daya, daidaitawa da inganta tsarin shigar da kudaden shiga, karuwar haraji zuwa GDP, da kawar da nauyin haraji kan talakawa.

“Tsarin raba haraji a yanzu kashi 15 ga Gwamnatin Tarayya, kaso 50, na jihohi, da kaso 35 na kananan hukumomi, ana ba da shawarar canzawa ya zamto Gwamatin Tarayya na da kashi 10, Jihohi 55, sai kananan hukumomi kuma su ja kaso 35,” in ji shi.

Wani lamari na daban kuma shi ne, batun sanya harajin kayan masarufi da wasu jihohi ke yi tare da BAT, hakan na kara wa ‘yan kasa nauyi tare da wahalhalu. Amma wannan sake fasalin na nufin dakatar da duk haraji ban da BAT.

A halin yanzu, rabon harajin BAT tsakanin jihohi ya dogara ne akan samun kashi 20, da kashi 50, da kuma kashi 30 na yawan jama’a.

Garambawul din da za a yi wa harajin bisa shawara, wani nau’i ne daban na cire kudi, wanda ya danganta yadda ake samarwa da kuma amfani da shi a maimakon yadda ake fitar da su, wanda a halin yanzu ya zama wata alfarma ce ga jihohi kananan hukumomi shalkwatocin kamfanunnuka.

A karkashin sabon tsarin,

Cire harajin zai kai kashi 60 na rabon BAT, don tabbatar da ingantaccen daidaito da kuma hana kowace jiha neman ba da harajin BAT a matsayin harajin jiha. Irin wannan matakin ba wai kawai zai haifar da raguwar kudaden shiga ga dukkan matakan gwamnati ba ne har ma da sanya wani nauyi ga ‘yan kasuwa.

Shugaban Hukumar Tara Haraji ta Kasa Zacch Adedeji, ya bayyana cewa, idan aka amince da shi a matsayin doka, sabon tsarin zai tabbatar da yin adalci ga jihohi ba tare da dogaro da manyan kamfanoni masu yawa ba kuma za su gane irin gudunmawar da suke bayarwa ga tattalin arziki.

Mista Adedeji ya kuma ba da tabbacin cewa sabon kudirin harajin ba zai zama barazana ga wanzuwar wata hukuma ko ayyuka na gwamnati ba.

Ya jaddada cewa babu daya daga cikin kudurorin haraji guda hudu da ke gaban majalisar dokokin kasar da yake barazana ga wanzuwar kowace hukuma da suka hada da Hukumar Kula Da Harkokin Kimiyya Da Kere-Kere ta Kasa (NASENI), da Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Kasa (NITDA), da kuma Babbar Hukumar Ilimi ka Kasa.

 

’Yan Majalisa Sun Goyi Bayan Tinubu

Majalisar Wakilai ta ce kudurin dokar sake fasalin haraji na da nufin yin amfani da kudaden shigar Nijeriya wajen inganta daidaito, da samar da yanayin da zai ba da damar zuba jari da kirkire-kirkire.

Kakakin majalisar wakilai Abbas Tajudeen ne ya bayyana haka ne a wani taro mai taken ‘Zaman Majalissar Dokokin Jama’a Kan Kudiri Gyaran Doka’ wanda majalisar ta shirya a Abuja ranar Litinin. Sai dai sun ce a matsayinsu na wakilan jama’a, dole ne ‘yan majalisar su tunkari sauye-sauyen cikin tunani tare da fahimtar tasirinsu ga kowane bangare na al’umma.

Wadannan sun hada da kudurin dokar harajin Najeriya na 2024, wanda ake sa ran zai samar da tsarin kasafin kudin haraji a kasar, da kuma dokar kula da haraji, wanda zai ba da fayyace kuma takaitaccen tsarin shari’a kan duk harajin kasar da kuma rage sabani.

Sauran sun hada da dokar kafa Hukumar Tattara Kudaden Shiga ta Nijeriya, wadda za ta soke dokar Hukumar Tara Haraji ta Kasa da Kuma kafa Hukumar Tattara Kudaden Shiga ta Nijeriya, da kuma dokar kafa Hukumar Tattara Haraji ta Hadin Gwiwa, wadda za ta kafa kotun sauraron kararrakin haraji da kuma mai kula da haraji.

Wadannan a yanzu haka suna gaban majalisar dokokin kasar wanda kuma sun haifar da cece-kuce.

Sai dai kakakin majalisar Abbas ya ce ya kamata haraji ya kasance akan gaskiya da adalci, tare da daidaita bukatun kudaden shiga na jama’a da nauyin da suke dora wa daidaikun mutane da ‘yan kasuwa.

Ya ce har yanzu majalisar ba ta dau takamaimiyar matsaya kan wadannan kudirori ba, domin aikinta shi ne ta yi nazari sosai da tabbatar da cewa sun yi daidai da maslahar al’ummar mazabarta da kasa baki daya.

Muna tare da Tinubu, ba gwamnoni ba – Agbese

Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Philip Agbese, ya ce ‘ya’yan jam’iyyar Green Chamber za su marawa shugaban Kasa Bola Tinubu baya kan kudirin sake fasalin harajin da za a yi wanda gwamnonin jihohinsu da ke son a janye dokar.

Agbese, a wata hira da ‘yan jarida a Abuja, ya ce ‘yan majalisar sun dauki kudirin a matsayin wani abin da zai kawo ci gaban tattalin arziki, don haka a shirye suke su yi watsi da kudurorin gwamnonin domin zartar da wadannan kudirori guda hudu.

Taiwo Oyedele

Da yake yi wa ‘yan majalisar tarayya bayani, Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa Kan Manufofin Kasafin Kudi Da Sake Fasalin Haraji, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa, kudirin sake fasalin harajin da ake shirin yi, ba wai an yi niyya ne don lalata wani yanki ko wani bangare na kasar nan ba.

Ya ce dokar da aka gabatar za ta tabbatar da inganci ne kawai tare da ba da karin kudaden shiga ga jihohin da ake amfani da kayayyaki da ayyuka.

Shugaban kwamitin shugaban kasa ya jaddada cewa babu wani abin tsoro a cikin kudirorin domin za su samar da maslaha ne ga Nijeriya musamman jihohi da kananan hukumomi. “Babu wani mummunan tunani game da kowane yanki ko wani abu,” in ji shi.

Dan Majalisar Wakilai daga Jihar Kano, Abdulmummin Jibrin

A nasa bangaren Dan Majalisar Wakilai daga Jihar Kano, Abdulmummin Jibrin, ya roki mutanen Arewa su mara wa kudurin dokar sake fasalin harajin baya da Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya kawo.

Dan majalisar ya bayyana hakan ne a yayin da yake magana a ranar Lahadi a cikin shirin talabijin na Channels.

Kofa ya ce kudurin na kunshe da abubuwa da dama da yankin Arewa za ta amfani da su.

“Kudurin ya kunshi wasu matakan ba wa jihohin Arewa kariya daga kowanne irin abin da ka iya cutar da su,”

“Wadannan matakai na da muhimmancin gaske wajen kare muradan yankin Arewa saboda ko da an sake fasalin harajin, Arewa ba za ta fuskanci wani kaluble ba,” in ji Jibrin Kofa.

Mataimakin Kakakin Majalisa

Shima a nasa bangaren, mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa, za a binciki kudirin gyaran harajin domin bai wa ‘yan kasar damar tantance su da kuma bayar da shawarwari.

’Yan majalisar Arewa za su kasance masu samar da maslahar kasa – Doguwa

Shugaban Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai na Yankin Arewa, Hon. Ado-Doguwa, wanda ya zanta da manema labarai a wajen taron garambawul din da majalisar ta shirya a Abuja ranar Litinin, ya ba da tabbacin cewa ba za su gaggauta aiwatar da tsarin ba, kuma za su yi adalci ga kudirin da kuma al’ummar Nijeriya ta hanyar yin nazari cikin tsanaki kafin a amince da su.

Dan majalisa daya tilo da ya kalubalanci kudirin Sanata Ali Ndume

A majalisar kuwa, sanata Ali Ndume, wanda ke wakiltar Barno ta Kudu, shi ne jagaba wajen kalubalantar kudurin.

A yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, Ndume, ya ce wannan kuduri ya makara domin ba wanda aka tuntuba a kai.

Har zuwa yanzu dai wannan kuduri yana kan matakin karatu na farko a majalisun kasar nan.

Haka ma ko da a watan da ya gabata, kwamitin kudi na majalisun sun zauna da shugaban hukumar tattara haraji na kasa domin duba lamarin.

Shugaban Hukumar Tara Kudaden Shiga Ta Kasa FIRS

A nasa bangaren, Shugaban Hukumar Tara Haraji Ta Kasa FIRS, Zach Adedeji, ya bayyana cewa, wannan kudiri zai amfani daukacin jihohi, ba tare da la’akari da yanayin tattalin arzikinsu ba.

LEADERSHIP ta tunatar da cewa shugaba Tinubu ya mika wa majalisar dokokin tarayya wasu kudirori guda hudu na yi wa haraji garambawul ga majalisar dokokin kasar domin tantancewa, biyo bayan shawarwarin da kwamitin shugaban kasa kan sake fasalin kasafin kudi da haraji, karkashin jagorancin Taiwo Oyedele ya bayar.

Haka kuma kungiyar Ulama ta kasa mai shalkwata a garin Kano ta fitar da sanarwar neman a sake nazari a kan shirion yi wa dokar haraji kwaskwarima. Takardfar sanarwa da aka buga a wasu manyan jaridun kasar nan tare da sa hannun shugaban tafiyar Alhaji Aminu Inuwa Muhammad da sakatarensa Injiniya Basheer Adamu Aliyu tare da kuma wasu manyan malamai 25 daga jihohin arewacin Nijeriya. A sanarwsa sun nemi a sake nazari tare da tattaunawa domin a tafi da kowa da kowa a maganar yi wa dokar harajin kwaskwarima dmin kada a yi kitso da kwarkwarta.

Haraji
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
Haraji
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Dokar Haraji Ta Gwamnatin Tinubu Za Ta Illata Arewa

Dokar Haraji Ta Gwamnatin Tinubu Za Ta Illata Arewa

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.