ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
JNIM

A ranar 31 na watan Oktobar 2025, Kungiyar ‘Yan Ta’adda ta Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimeen JNIM, ta yi ikirarin cewa, ta kaddamar da kanta cikin kasar nan.

Wannan ikirarin na ta, ya nuna tsagwaron sakacin da aka yi a fannin tsaron kasar, musamman duba da yadda kungiyar, masu tsatsauran ra’ayi, har suka iya  kutse a cikin kasar.

  • Akwai Bukatar Karfafa Hadaka Domin Ciyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa Gaba A Afirka —Dantsoho
  • Sin: Kome Zai Samu Yankin Taiwan Babu Ruwan Kasar Japan

Kungiyar wadda ke da akida irin ta Kungiyar Ta’addanci ta Al-Kaeda, ta shelanta cewa, ta hallaka Sojin kasar daya, yayin da ‘ya’yanta, suka yi wa tawagar dakarun soji, kwanton Bauna a Iyakar kasar Benin.

ADVERTISEMENT

 

Kazalika, wannan kutsen na kungiyar, ya nuna karara na irin sakacin tsaron kasar nan da har ayyukan kungiyar, ya tsallake yankin Sahel zuwa Afrika ta Yamma.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

 

Za a iya cewa, ta yi wannan kusten daidai da lokacin da Nijeriya, ke ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro da kuma yadda wasu kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi ke kai hare-hare kan wasu ‘yan kasar.

 

A nan, wannan Jaridar na yin mamaki kan yadda kungiyar ta As JNIM mai alaka da Al-Kaeda ke kara ba za ayyukanta a cikin kasar.

A saboda hakan Jaridar na ganin ya zama wajbi mahukuntan tsaron kasar, da su tabbatar da sun karfafa tsaro, a iyakokin kasar

Kungiyar ta JNIM, an kirkiro da ita ne, a watan Maris na 2017, wadda kuma ta yi hadaka da kungiyar Al-Kaeda.

Bugu da kari, Majalisar Tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya, ta ayyana kungiyar ta JNIM, a matsayin wani reshe na Al-Kaida, da ke a kasar Mali.

Zallaka, Gidauniyar kafar yada labarai ta JNIM, ta yi wallafa ikirarin cewa, dakarun kungiyar sun samu nasarar yiwa sojojin kwanton Bauna ta hanyar dasa Bam a Iyakar Benin, wanda hakan, ya janyo mutwar soja daya.

Wannan ayyukan ta’addancin kungiyar, ya yi daidai da, irin salon da ta yi watan Yulin 2025, wanda ta kai hare-haren da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 54 a kasar Burkina Faso, wasu 36 a kasar Mali, da kuma wasu bakwai, a Jamhuriyyar Nijar, ta hanyar yin amfani da Iyakar Markoye.

Kazalika, kungiyar na yin amfani da Jirage marasa matuka, wajen kai hare-harensu, wadda kuma Al-Kaeda ce, ke tallafa wa mata da makamai da kuma kudade, domin aikata ta’asarsu.

Iyakar Benin da Nijeriya, ta kasance, wata mashiga ta yin fasakwarin makamai da muggana kayan maye, wanda hakan ya zama babbar hanyar da kungiyar ke yin amfani da ita.

Wani rahoton ta UNODC ta fitar a 2025 ya nuna cewa, an kiyasta cewa, an shigo da kaso 70 na kananan makamai ta Iyakar Benin da Nijeriya,

Hakazalika, wani rahoton Bankin Duniya ya sanar da cewa, talauci, ya Arewacin Nijeriya, ya sanya irin wadannan kungiyoyin ta’addacin daukar hayar wasu shiga cikin irin wadannan kungiyoyin ta’addancin.

Wannan Jaridar na da yakin cewa, domin a dakile ayyuan kutsen irin wadannan kungiyoyin ta’addancin, ya zama wajbi mahukunta a kasar nan, su amfani da kimiyyar fasahar zamani wajen tabbatarwa da karfafa tsaro, a iyakon kasar.

Bugu da kari, ya zama wajbi, a sanya na’urorin zamani na sanya ido da kuma yin amfani da Jiragen sama, marasa matuka domin tabbatar da tsaro.

Kazalika, ya kamata mahukuntan kasar, su yi koyi da salon da jihar Sokoto ta kirkiro da shi, na karrarfafa tsaro a iyakokin jihar.

Ya kuma kamata a yi amfani da salon kungiyar ECOWAS, na gudanar da aikin sintiri na hadaka domin dakile shigorar ‘yan ta’adda daga yankin Sahel inda kwararowarsu, ta kai kaso da shigo da makamai, ta kai 60.

Bugu da kari, akwai bukatar a zuba kudade masu dimbin yawa a shekarar 2026, cikin Cibiyar Dakile Shigo da Kananan Makai ta kasa, tare da kuma tabbatar da ana yin aiki kafada da kafada a tsakanin Hukumomin Tsaro, musaman domin a dakile kutsen kungiyoyin ‘yan ta’adda zuwa cikin kasar nan.

Haka, ya kamata mahukunta a kasar, su kirkiro da shirye-shiye a cikin alumma, kamar dai a jihar Borno, domin a bai wa matasa horon koyon sana’aion hannu domin kare su, daga jan ra’ayin kungiyar ‘yan ta’adda na shiga cikin kungiyoyin.

Da irin wannan salon jan ra’ayin wasu matasan ne, har ta kai ga kungiyar Al-Kaeda ta yi fice, wajen janyo matasa a cikinta.

Wasu daga cikin kwararru, musamman da ke yin fashin baki kan aukuwar rikice-rikice, suna ganin yin yafiya ga ‘yan ta’adda da suka tuba suka kuma ajiya makamansu, hakan zai taimaka, wajen rage aikata ta’addanci.

Duba da yadda kungiyar ta JNIM da ke da alaka da Al-Kaeda, ta yi kutse a cikin kasar nan, ya zama wajbi, mahukunta a kasar, su dauki matakan gaggawa domin a taka mata birki, wanda hakan zai bai wa kasar samun cikakken ikon bai wa iyakon kariya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mutane 7 Ne Suka Rasu Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro Da Taifod Ba Wata Sabuwar Cuta Ba – Gwamnatin Kano
Ra'ayinmu

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

November 28, 2025
Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
JNIM
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Next Post
Yunkurin Japan Na Komawa Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Japan Na Komawa Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ba Zai Yi Nasara Ba

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.