ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

by Leadership Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Kano

Ci gaba da samun karuwar hare-hare kan al’umomin da ke a garurunwan iyaka da jihar da wasu jihohi, lamarin na kara jefa fargaba a cikin jama’a.

A saboda haka, akwai matukar bukatar a hada karfi da karfe, domin a kawo karshen kalubalen rashin tsaro, da tuni, ya zamowa kasar tamkar wani karfen Kafa, musamman a jihohin da ke a Arewa ta Yamma da kuma a jihohin da ke a Arewa ta Tsakiya

  • Tinubu Da Shugabannin ECOWAS Sun Gudanar Da Taron Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau
  • Sarkin Musulmi Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Kazalika, wasu alumomin da ke a jihohi kamarsu, Zamfara, Katsina, Kebbi da Sokoto, na ci gaba da kokakwa, kan yawan hare-haren da ‘yanbindiga ke kai masu, ind hare-haren, suka auka a wasu yankuna na Shanono da ke a Kano, wanda suke da iyaka da, musamman Katsina.

ADVERTISEMENT

Sai dai, wasu da ke a cikin alummomin na garin Shanono, sun tabbatar da cewa, tun a 2022 ne, ake kai masu hare-haren, inda a yayin hare-haren, aka kashe wasu, wasu kuma aka tarwatsasu daga matsugunansu, wasu kuma aka sace Sahnunsu.

Hakazalika, abin bakin ciki ne, kan samu karuwar hare-haren a Tsanyawa, Shanono, Bagwai, Gwarzo, da Karaye, da ke a iyaka da Katsina, inda lamarin, ya kuma ba zu, daga Katsina zuwa Kano.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

Bugu da kari, an ci gaba da samun karuwar kai hare-hare da kuma yin garkuwa da mutane a yankin  Faruruwa da ke karamar hukumar Shanono, wanda har da wasu mata da aka sace.

Aukuwar hare-haren, sun sanya alumomin da ke a yankunn Tudun Fulani, Malami, Unguwar Kudu, ’Yan Kwada, Santar Abuja, Kulki, Unguwar Tsamiya da Goron Dutse, da sauransu, tserewa, daga matsugunansu.

Wani abin takaicin shi ne, duk da yin yarjejeniya samar da zaman lafiya da wasu alumomin da ke a jihar Katsina, inda akalla kananan hukumomi 18, suka kulla wannan yarjejiniar da ‘yan bindigar, amma sai hare-haren, suka kara zafafa.

Ayar tambaya a nan ita ce, idan har da gaske ne, wannan yarjejeniyar, da gaske ne, amma mai ya sanya, ‘yan bindigar suka karkatar da Akalarsu,  zuwa kai hare-hare a jihar Kano?

Hakan ya nuna a zahairi cewa, kulla yarjejeniyar da ‘yan bindigar tamkar alumomin, sun hakawa kawunansu, wani Kabari ne.

Karin wani abin dubi shi ne, yadda daukacin ‘yanbindigar, suka halarci wajen kulla yarjejeniyar,  sabe da muggan makamansu, a kafada.

Mun sha fada ba tare da wata tamtama ba cewa, mafita kan wannan matsalar ta rashin tsaron shi ne, hukumomin tsaron kasar, su kara kaimi wajen kai hare-hare kan ‘yan bindigar, domin kawo karshen ayyukansu na rashin imani.

Idan har mahukunta suka ci gaba da yin sakaci kan ci gaba da samun karuwar ayyukan ‘yanbindigar a Kano, ba fata ba, idan ba a yi a hankali ba, lamarin zai iya munana, fiye da na jihohin Zamfara, Kebbi da Katsina.

Maganar gaskiya, ci gaba da samun karuwar hare-haren ‘yanbindigar kan alumomin da ke a iyakar Kano, hakan ya nuna cewa, ya zma waji, a tashi ka’in da na’in, domin tunkarar kalubalen na rashin tsaron.

Shin me ya sa, yake zama wahala ga jami’an tsaro, tare da hadaka da gwamnatocin da ke a Arewa ta Yamma, suka gaza hada karfi da karfe domin kawo karshen ayyukan na ‘yanbidiga da kuma aikata, suran manyan laifuka a jihohin?

A nan, za mu iya cewa, ga dukkan lamu, rashin yin hobbasan gwamnatocin da ke a wadannan jihohin na tunkarar matsalar ne, ya kara bai wa ‘yanbindigar karfin ci gaba da aikata, ta’asarsu, a jihohin.

Lokaci ya yi da gwamnatocin da ke a wadannan jihohin za su tashi kan jiki kan karfi, domin magance kai hare-haren da ke akuwa kan alumomin da ke zaune a iyakon su, musamman ta hanyar hada hannu da sauran hukumomin tsaro, domin a cimma wannan nasarar.

Bugu da kari, ya zama wajbi, gwamnatocin wadannan jihohin, su mayar da hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin alumomin su, daga hare-haren na ‘yan bindigar, wadanda har yanzu, suke ci gaba da cin Karensu, babu babbaka.

Kazalika, duba da yadda hare-haren na ‘yanbidagar ya durkusar da tattalin arzikin alumomin da ke a yankin, ya zama wajbi, gwamnatocin da ke a wadannan jihohin, su lalubo da mafita kan kalubalen na rashin tsaron.

Ra’ayin wannan Jaridar a nan shi ne, ya zama wajbi gwamnatocin da ke a wadannan jihohin, su tashi tsaye wajen, musamman duba da cewa, a yanzu, an shigo cikin kakar rani ne, wanda hakan zai sanya jami’an tsaro, da ke ci gaba da yakar ‘yanbindigar, samun damar kutsawa har zuwa sansanonin ‘yanbindigar domin ragargazarsu.

Lokaci ya yi da za a kawo karshen wannan zubar da mutuncin kasar da ‘yanbidigar ke ci gaba da yi, a idon duniya, musamman a yankunan da suka yi kaka gida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya
Ra'ayinmu

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

November 21, 2025
Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Kano
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Next Post
Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.