• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Karuwar Talauci A Nijeriya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Dalilan Karuwar Talauci A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A watan Fabrairu na wannan shekarar, fusatattun matasa suka mamaye titunan garin Minna babban birnin Jihar Neja da wasu kuma matasan a Kano da suka gudanar da zanga-zanga a kan abin da suka kira tsadar rayuwa a kasar nan.Irin wannan zanga-zangar ta kuma barke a Jihar Ondo da wasu sassan kudu masu yammacin kasar nan.

Kungiyoyin addini sun lura da cewa rayuwa ga talaka a Nijeriya tana kara tsauwwala musamman abin da ya shafi farashin kayan abinci da kudin sufuri da kuma sauran al’amurran yau da kullum duk suna neman su gagari yawancin ‘yan Nijeriya.

  • Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu
  • Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi

Kungiyar Kiristoci ta kasa CAN ta bayyana cewa, al’amarin yana kara ta’azarra ne sakamakon matsalar tsaro da ake fama da ita wanda kuma shi ya haifar da kashe-kashe da kuma garkuwa da mutane don mena kudin fansa.

Idan za a iya tunawa, wannan jaridar ta ruwaito cewa, mai alfarma Sultan na Sakkwato, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar lll wanda kuma shi ne shugaban kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) ya bukaci gwamnatocin tarayya da na jihohi su gaggauta kawo dauki domin magance matsalar tsadar rayuwa wadda ita ce ta tunzura al’umma yin zanga-zanga a wasu sassan Nijeriya.

Kasar nan tana fuskantar matsanancin  tattalin arziki da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin Nijeriya, al’umma na fama da talauci da tashin hankali a kowane lungu da sako na kasa.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

A yayin da wannan gwamnatin ke neman cika shekara daya da dare wa kan karagar mulki,mun lura cewa,babu wani abin da ya canja a cikin wannan shekarar sai da karin talauci da yunwa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Shugaban kasa Tinubu ya janye tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayu 2024 yayin da aka tanstar da shi a matsayin shugaban kasa daga nan farashin man fetur ya yi tashi da ninkin baninkin 300 hakan kuma shi ya haifar da hauhawar farashin kayan abinci da sauran kayan amfani na yau da kullum.

Karuwar farashin man fetur da aka samu ta haifar da tsadar kayayyakin aiki ga kamfanoni da kuma kudin zirga-zirga haka kuma ya kai ga dora wadannan kudaden a kan talakawa masu amfani da kayan da kamfanonin ke sarrafawa.

Karuwar yanwa ta kuma haifar da tashin hankali a tsakanin matasa, har an fara samun fusasasstun matasa da suke tare hanya suna wasoson kayan abinci, dukkan wadannan kuma sakamakon tsare-tsare ne na Shugaban Kasa Bola Tinubu, musamman tsarinsa na karya darajar naira.

Sakamakon wadannan manufofin ne na tsare-tsaren tattalin arzikin Shugaba Tinubu ya haifar da matsanancin wahalar rayuwa ga al’ummar Nijeriya gaba daya.

Farashin kayan masarufi sun yi tashin gwauron zabo, kayan abinci kamar shinkafa,wake, masara tumatur da sauransu sun tashi da kashi 25.34 zuwa 40.01 a kididdigar da aka yi a watan Maris na shekarar 2024.

Ana cikin wannan matsin ne na tattalin arzikin sai kuma ga shi gwamnati ta kara kudin wutar lantarki da kashi 603 inda ya zama naira 225 a kan kilowat daya.

Duk da wannan karin ba wai ana samun wutan lantarkin yadda ya kamata ba ne,hakan kuma ya kai durkushewar kananan masana’antu da dama.

Babu ko kokwanto, mastalar tattalin arzikin da ake fama da ita a halin yanzu, tsanannin talauci da tsadar farashin abinci suna yin barazana ga rayuwar talakan Nijeriya.

Tsadar rayuwa na ci gaba da takura ‘yan Nijeriya,musamman matasa wadanda ke hankoron barin kasar domin samun ingantaccen rayuwa a kasashen waje.

A wani binciike da wata kungiya mai zaman kanta mai suna NOIPolls ta gudanar a watan Agusta na 2024 ta gano cewa kashi 63 na ‘yan Nijeriya a fadin kasar nan a shirye suke su yi kaura zuwa kasashen waje in sun samu damar yin haka.

Binciken ya kuma gano cewa matasa masu shekaru tsakanin 18 zuwa 35 sune a kan gaba wajen neman hanyar yin kaura zuwa kasashen waje.

Binciken ya kuma gano cewa, kashi 60 na masu neman fita kasashen waje suna yi ne domin samun ingantacciyar rayuwa a kasashen waje.

Amma kashi 3 na masu hankoron fita sun bayyana matsalar tsaro a matsayin dalilin su na neman fita kasashen waje.

A halin yanzu yunwa da matsalar tsaro na ci gaba da wahalar da ‘yan Nijeriya sai kuma ga hauhawar farashi ya kara kunno kai,tabbas al’umma na cikin wahala a Nijeriya.

Duk bangaren da ka duba a Nijeriya zaka lura da yadda garkuwa da mutane, ta’addanci, harkokin ‘yan bindiga suke aukuwa a kullum garin Allah ya waye.

Ci gaba da tabarbarewar darajar naira da kuma yadda gwamnati ta kasa shawo kan lamarin ya kara jefa ‘yan Nijeriya cikin halin ni ‘yasu.

Yayin da lamarin yake kara ta’azzara,dole gwamnati ta gaggauta daukar matakan ta yin maganin matsalar tattalin arzikin da ake fuskanta da kuma matsalar tsaro a sassan Nijeriya wadanda sune suka haifar da tsadar rayuwa ga talakawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NijeriyaTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu

Next Post

Noman Daminar Bana: Kisan Manoma Na Mayar Da Hannun Agogo Baya

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

3 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

6 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

10 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

13 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

22 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

1 day ago
Next Post
Noman Daminar Bana: Kisan Manoma Na Mayar Da Hannun Agogo Baya

Noman Daminar Bana: Kisan Manoma Na Mayar Da Hannun Agogo Baya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.