ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ECOWAS Ta Gargadi Sojin Nijar A Kan Hukunta Bazoum

by Sadiq
3 years ago
ECOWAS

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS), ta ce ta kadu da jin yunkurin sojoji masu juyin mulki a Nijar na tuhumar zababben shugaban kasa Bazoum Mohamed da zargin babbar cin amanar kasa.

Wata sanarwa da kungiyar ta fitar sa’o’i bayan kalaman sojojin na yi wa Bazoum shari’a, ECOWAS ta ce matakin wani takalar fada ne daga shugabannin sojin.

  • NIS Ta Yi Gargadi Kan Ma Su Balaguro Ta Haramtacciyar Hanya
  • Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Ta kuma ce hakan ya ci karo da rahotannin da ake yadawa cewa sabbin masu mulkin Nijar din sun nuna sha’awar bin hanyar masalaha don kawo karshen dambarwar da ake ciki.

ADVERTISEMENT

Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar sun ce sun tattara isasshiyar shaidar za a iya gurfanar da hambararren shugaban ksar Bazoum Mohamed a gaban kotu, bisa laifin cin amanar kasa.

Sun kuma tuhume shi da yi wa tsaron cikin gida da na wajen kasar, zagon kasa.

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Kakakin sojin Kanal Amadou Abdramane ne, ya bayyana haka a wani jawabi da ya yi ta tashar talbijin ta kasar.

Sojojin na tsare da Bazoum da iyalansa a wani daki na karkashin kasa a fadar gwamnati da ke birnin Yamai, tun bayan hambarar da shi a ranar Lahadi 26 ga watan Yulin bana.

Baya ga shugaban sojojin sun kuma kama wasu daga cikin jiga-jigan gwamnatinsa da ma na jam’iyyarsa ta PNDS Tarayya.

Mai magana da yawun gwamnatin sojin ya ce tuni sun riga ma sun tattara duk wasu bayanai da shaidun da suke bukata domin gurfanar da Bazoum a gaban shari’a.

A sanarwar, kakakin ya ce, za su gurfanar da Bazoum tare da wadanda ya kira masu hada baki da shi a cikin kasar da ma ketare a kan laifukan da suka zayyana, saboda musayar bayanan da ya yi tsakaninsa da wasu ‘yan kasashen waje da shugabannin kasashe da kuma shugabannin kungiyoyin kasashen duniya.

Bayan karbe mulki tare da rushe zababbiyar gwamnatin tuni suka nada majalisar ministoci, tare da yin biris da duk wani kira na neman sasanta rikicin ta hanyar diflomasiyya, daga ECOWAS da sauran kasashe da hukumomi masu rajin kare dimokradiyya na duniya.

MASU ALAKA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
Manyan Labarai

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Next Post
‘Yan Majalisar Ghana Sun Gargadi Shugaban Kasar Kan Tura Sojoji Nijar

'Yan Majalisar Ghana Sun Gargadi Shugaban Kasar Kan Tura Sojoji Nijar

LABARAI MASU NASABA

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.