ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fatan Samun Kwanciyar Hankali Da Wadata A Dangantakar Dake Tsakanin Sin Da Australia

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

Akwai kyakkyawar alaka tsakanin tattalin arzikin Australiya da tattalin arzikin kasar Sin, inda Sin ta dauki kusan kashi daya bisa uku na dukkan kayayyakin ficen Australiya a shekarar 2023, sa’annan hajojin Sin sun kai sama da kashi daya bisa hudu na kayayyakin shigen Australia. Don jaddada muhimmancin dangantakar, firaministan Australiya Anthony Albanese ya bayyana a wannan shekarar cewa, “daya cikin hudu na ayyukan yi a Australiya ya dogara ne a kan kasuwanci, kuma daya cikin hudu na dalar da Australiya ke samu na kayayyakin fice daga cinikayya ce da kasar Sin.”

Australiya ta kasance cikin koma bayan tattalin arziki na kan kowanne mutum wato per capital a shekarar 2023. Ma’ana, yayin da tattalin arzikinta ke ci gaba da bunkasa, yawan al’ummarta na karuwa da sauri fiye da tattalin arzikin. A halin yanzu tattaunawa kan tattalin arzikin kasar ta fi mai da hankali kan matsalar tsadar rayuwa, yayin da karin talakawan Australiya ke bukatar abinci mai yawa, da gidaje da kudaden amfani wadanda ke tasiri ga rayuwar yau da kullun a kasar.

  • Alamomi 20 Na Ciwon Kansa Da Suka Kamata A Sani
  • Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Afrika ta Kudu

Bisa wadannan dalilan ne Australiya take fatan ingantuwar dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin za ta haifar da wani fa’ida ta fuskar tattalin arziki don taimakawa magance wadannan yanayi. Muhimmin aiki ga bangarorin biyu zai kasance nemo hanyoyin zurfafa dangantakar cinikayya, da kirkirar sabbin hanyoyin hadin gwiwa, a fannin habaka ababen hawa na lantarki (EV) a Australiya, saboda kasar Sin ita ce kan gaba a duniya a fasahar EV, tana da kuma masana’antu wadanda suka yi matukar dacewa da matsayin Australiya a matsayin kasa mafi girma wajen samar da lithium a duniya. Yayin da kasashen biyu suka kuduri aniyar aiwatar da manufofin rage hayakin carbon mai gurbata muhalli, ba abin mamaki ba ne cewa wani bangare na ziyarar firaministan kasar Li ya hada da ziyarar jihar yammacin Australiya wadda ta mai da hankali kan hakar ma’adinai.

ADVERTISEMENT

Ziyarar ta firaminista Li kuma ta zo a daidai lokacin da amincewar jama’ar Australiya ga Amurka ta ragu matuka, inda wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da cibiyar Lowy ta gudanar a baya-bayan nan ta nuna cewa kashi 56 cikin 100 na jama’ar Australiya ne kawai suka amince da Amurka wajen yin abin da ya dace idan aka kwatanta da kashi 61 cikin 100 na bara. Wannan wata alama ce da ke nuna cewa al’ummar Australiya na fahimtar hakikanin fa’idar dunkulewar kasashen duniya, saboda haka, bukatar aiwatar da manufofin ketare mai cin gashin kanta, na tabbatar da alakar aiki tsakanin Australiya da kasar Sin ya zama wani muhimmin bangare.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK

MASU ALAKA

Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya
Daga Birnin Sin

Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

September 17, 2026
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

September 17, 2026
Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

September 17, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Nemi Karin Tallafi Ga Manyan Makarantun Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Nemi Karin Tallafi Ga Manyan Makarantun Jihar

LABARAI MASU NASABA

ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

September 18, 2026
Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

September 18, 2026
Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

September 18, 2026
Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

September 18, 2026
Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

September 18, 2026
Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

September 17, 2026
U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

September 17, 2026
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

September 17, 2026
Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

September 17, 2026
Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

September 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.