ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
51 minutes ago
Bala Mohammed

Gwamnatin Jihar Bauchi ta bayyana wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, wanda ke iƙirarin cewa Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed ya amince da kayyade sadakin Zawarawa zuwa naira 1,500, a matsayin ƙarya tsagwaronta da wasu suka ƙirƙiro domin sanya ruɗani a zukatan al’umman jihar.

Bidiyon, wanda ya bazu sosai a shafukan Facebook da TikTok, ya kuma yi zargin cewa Sarkin Sayawa (Gum Zar) ya umarci al’ummar yankin da su bi wannan sabuwar tsarin da gwamnati ta ɓullo da shi.Haka kuma, wani mai amfani da kafar sada zumunta mai suna Boroh James Hussaini ya wallafa cewa sadakin budurwa da ta taɓa haihuwa ba tare da aure ba zai kasance Naira 3,000, yayin da matan da suka daɗe ba su yi aure ba kuma ba su taɓa haihuwa ba za a aurar da su ga direbobi ba tare da an biya sadaki ba.

Da ya ke ƙaryata batun yayin ganawa da manema labarai a Bauchi ranar Asabar, Kwamishinan kula da harƙoƙin addini, Injiniya Muhammad Binni Abdulkadir, ya bayyana waɗannan iƙirari a matsayin ƙirƙirarru, marasa tushe balle makama kuma karya ce gaba ɗaya.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa Gwamnatin Jihar Bauchi ba ta taɓa ƙirƙirar ko amincewa da wata manufa da ta shafi kayyade sadakin matan da aka sake su ko kuma mata marasa aure ba, yana mai cewa an ƙirƙiri waɗannan rahotanni ne da gangan domin ruɗar da jama’a.

Kwamishinan ya buƙaci al’ummar jihar da su yi watsi da waɗannan jita-jita, tare da gujewa yaɗawa ko kambama bayanan da ba a tantance ba, domin hakan na iya haifar da ruɗani da tashin hankali ba tare da wani dalili ba.

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Ya ƙara da cewa tun daga lokacin da ya hau mulki, Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed ya kasance mai mutunta koyarwar addini, al’adun gargajiya da kyawawan ɗabi’un al’ummar Jihar Bauchi.

Injiniya Binni ya kuma yi kira ga jama’a da su tabbatar da sahihancin duk wani bayani kafin su yaɗa shi a kafafen sada zumunta, yana gargaɗin cewa yaɗa labaran ƙarya na iya yin illa ga zaman lafiya, haɗin kai da martabar Jihar Bauchi, tare da lalata kyawawan al’adunta da gadon addininta.

Sadaki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
  • Sulaiman
    Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna
  • Sulaiman
    Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
Sadaki
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara
Labarai

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026

LABARAI MASU NASABA

Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.