Gwamnatin Jihar Bauchi ta bayyana wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, wanda ke iƙirarin cewa Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed ya amince da kayyade sadakin Zawarawa zuwa naira 1,500, a matsayin ƙarya tsagwaronta da wasu suka ƙirƙiro domin sanya ruɗani a zukatan al’umman jihar.
Bidiyon, wanda ya bazu sosai a shafukan Facebook da TikTok, ya kuma yi zargin cewa Sarkin Sayawa (Gum Zar) ya umarci al’ummar yankin da su bi wannan sabuwar tsarin da gwamnati ta ɓullo da shi.Haka kuma, wani mai amfani da kafar sada zumunta mai suna Boroh James Hussaini ya wallafa cewa sadakin budurwa da ta taɓa haihuwa ba tare da aure ba zai kasance Naira 3,000, yayin da matan da suka daɗe ba su yi aure ba kuma ba su taɓa haihuwa ba za a aurar da su ga direbobi ba tare da an biya sadaki ba.
Da ya ke ƙaryata batun yayin ganawa da manema labarai a Bauchi ranar Asabar, Kwamishinan kula da harƙoƙin addini, Injiniya Muhammad Binni Abdulkadir, ya bayyana waɗannan iƙirari a matsayin ƙirƙirarru, marasa tushe balle makama kuma karya ce gaba ɗaya.
Ya jaddada cewa Gwamnatin Jihar Bauchi ba ta taɓa ƙirƙirar ko amincewa da wata manufa da ta shafi kayyade sadakin matan da aka sake su ko kuma mata marasa aure ba, yana mai cewa an ƙirƙiri waɗannan rahotanni ne da gangan domin ruɗar da jama’a.
Kwamishinan ya buƙaci al’ummar jihar da su yi watsi da waɗannan jita-jita, tare da gujewa yaɗawa ko kambama bayanan da ba a tantance ba, domin hakan na iya haifar da ruɗani da tashin hankali ba tare da wani dalili ba.
Ya ƙara da cewa tun daga lokacin da ya hau mulki, Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed ya kasance mai mutunta koyarwar addini, al’adun gargajiya da kyawawan ɗabi’un al’ummar Jihar Bauchi.
Injiniya Binni ya kuma yi kira ga jama’a da su tabbatar da sahihancin duk wani bayani kafin su yaɗa shi a kafafen sada zumunta, yana gargaɗin cewa yaɗa labaran ƙarya na iya yin illa ga zaman lafiya, haɗin kai da martabar Jihar Bauchi, tare da lalata kyawawan al’adunta da gadon addininta.













