• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Mutum 17 Don Mika Mulki Ga Gwamnati Mai Jiran Gado

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Mutum 17 Don Mika Mulki Ga Gwamnati Mai Jiran Gado
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar zartaswa ta Jihar Kano ta amince da kafa kwamitin mika mulki na mambobi 17 ga gwamnati mai jiran gado a jihar.

Majalisar ta kuma amince da wani karamin kwamiti mai mutum 100 wanda za a fitar da kundin tsarin mulki daga ma’aikatu da hukumomi daban-daban a jihar.

  • EFCC Ta Damke ‘Yan Damfarar Intanet 17 A Benue
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 2 A Jami’ar Zamfara

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a ranar Lahadi.

Ya ce kwamitin wanda ke karkashin jagorancin sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Usman Alhaji yana da wadannan mambobi a matsayin shugaban ma’aikatan gwamnati, babban lauya/kwamishanan shari’a, kwamishinan yada labarai, kwamishinan muhalli, kwamishinan kasuwanci.

Sauran sun hada da kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi, kwamishinan kananan hukumomi, kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa, kwamishinan kudi, kwamishinan ilimi da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Malam Garba ya bayyana cewa, babban kwamatin zai yi aiki cikin jituwa da nufin mika mulki cikin makonni uku.

Kwamishinan ya bayyana cewa an bai wa babban kwamitin rikon kwarya umarnin fara shirin mika mulki tare da rubuta nasarorin da aka samu a cikin wa’adin mulki biyu na gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.

Ya ce kwamitin zai kuma samu tare da tantance rahotanni daga ma’aikatu dangane da manyan nasarorin da aka samu, gami da ayyuka da tsari da ke gudana dangane da matakin aiwatar da kasafin kudi, matsaloli da dai sauransu.

Malam Garba ya yi nuni da cewa, an dora wa kwamitin alhakin daidaitawa da gudanar da ayyukan karamin kwamitin kan mika mulki, tattarawa da hada rahotonsu tare da mika rahoton mika mulki ga gwamnati mai zuwa cikin makonni hudu bayan kaddamar da shi.

Ya ce gwamna Ganduje zai kaddamar da kwamitin a ranar Talata da misalin karfe 2 na rana a dakin taro na ‘Africa House’ da ke gidan gwamnatin Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GandujeGwamnatin KanoGwamnatin Mai Jiran GadoKwamitiMika MulkiMuhammad Garba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Kwadibuwa Na Sa Ran Za A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Kasarsa Da Sin

Next Post

‘Yansanda Sun Mika Wa Almajiran El-Zakzaky Motocinsu Da Aka Kama

Related

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

4 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

19 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

1 day ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Mika Wa Almajiran El-Zakzaky Motocinsu Da Aka Kama

'Yansanda Sun Mika Wa Almajiran El-Zakzaky Motocinsu Da Aka Kama

LABARAI MASU NASABA

aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.