ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci – Marafan Gonin Gora

by Abubakar Abba
2 years ago
Farashin

Marafan Gonin Gora da ke a karamar hukumar Chikun a Jihar Kaduna, Alhaji Kabir Abubakar Danladi ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya na da laifi kan hauhawan farashin kayan masarufi a kasar nan.

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a Kaduna, basaraken ya yi nuni da cewa laifin gwamnatin shi ne, rashin shiga a cikin al’amuran ‘yan kasuwar kasar nan don ta taka musu birki.

  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Neman Zama Madaukakiya Tare Da Sake Waiwayar Dokokin Kasa Da Kasa

Alhaji Kabir wanda kuma shi ne shugaban kungiyar da ke wanzar da zaman lafiya a tsakanin matasa, ya ci gaba da cewa kamar yadda ‘yan kasuwar ke fakewa da tashin farashin dala suna kara farashin kayan, kamar yadda kowa ya sani, dala tana hawa ne tana sauka, wasu ‘yan kasuwar, musamman kanana ba masu taba ganin dalar ba.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, kamata ya yi idan farashin dalar ya sauka, suma ‘yan kasuwar sai su rage farashin kayansu, amma a kasar nan duk abun da farashinsa ya karu ba fa zai kara saukowa ba.

Kazalika, Kabir ya ce ‘yan kasuwar suna amfani da wannan damar ce don su tara abun duniya, inda ya ci gaba da cewa, kayan da ‘yan kasuwar ke sawo har yanzu suna nan a cikin shagunansu tsawon watanni.

LABARAI MASU NASABA

Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau

Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?

Ya ce, abun bakin ciki idan sun tashi sai su sayar da su a matsayin sabon farashin, idan ka yi masu magana sai su ce maka ai sun sawo kayan ne a sabon farashi.

Ya ce a lokacin mulkin soji na tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari an kayyade farashin kayan masarufi, haka ya kamata a wannan mulkin na dimokiradiyya ana da damar a yi hakan, domin ‘yan Nijeriys ne suka zabi gwamnatin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau
Labarai

Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau

December 14, 2025
Sojojin somaliya
Manyan Labarai

Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?

December 14, 2025
Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

December 13, 2025
Next Post
Daminar Bana: Manoma Su Guji Shuka Da Wuri, Su Rungumi Inshora – Masu Ruwa Da Tsaki

Daminar Bana: Manoma Su Guji Shuka Da Wuri, Su Rungumi Inshora – Masu Ruwa Da Tsaki

LABARAI MASU NASABA

Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau

Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau

December 14, 2025
Wacce Kasa Ce Za Ta Lashe Gasar Kofin Afirka

Yadda Haaland Ya Zura Kwallaye 100 A Firimiyar Ingila

December 14, 2025
Sojojin somaliya

Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?

December 14, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo 

Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo 

December 13, 2025
Sin Ta Karbi Shaidu Daga Rasha Dangane Da Tawagar Aikin Sojin Japan Mai Lamba 731

Sin Ta Karbi Shaidu Daga Rasha Dangane Da Tawagar Aikin Sojin Japan Mai Lamba 731

December 13, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Karatun Baya Dangane Da Tarihi Shi Ne Abun Da Ya Kamaci Japan

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Karatun Baya Dangane Da Tarihi Shi Ne Abun Da Ya Kamaci Japan

December 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa

December 13, 2025
Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin

Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin

December 13, 2025
Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing

Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing

December 13, 2025
Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

December 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.