Sakamakon wasu alkaluman jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta fitar, ya nuna yadda masu bayyana ra’ayoyi na kasa da kasa ke ganin dacewar kasar Japan ta yi karatun baya, dangane da tarihin abubuwan da suka faru a baya.
Alkaluman sun nuna kaso 82.7 na masu bayyana mahangarsu na ganin Japan za ta iya yin nasarar komawa cikin harkokin kasa da kasa ne kadai, idan ta amince da laifukan yaki da ta tafka a baya, ta kuma kawar da tunani irin na amfani da karfin soji.
Kasar Japan ta kaddamar da yakin danniya kan kasar Sin da wasu kasashen nahiyar Asiya, ta fakewa da wai “Dakile yanayin barazanar dorewarta”, matakin da ya zamo daya daga abubuwa mafiya muni da suka faru a tarihin bil’adama.
Kuri’un jin ra’ayoyin sun nuna yadda kaso 89.4 bisa dari na masu fadin albarkacin bakinsu, suka shaida kasancewar Japan kasa da ta tayar da yakin muzgunawa wasu kasashe a tarihi, suna masu ganin ya dace kasar ta rika taka-tsantsan wajen furta kalamai, da aiwatar da manufofi dangane da batutuwan na tarihi. Kazalika, kaso 90.4 bisa dari na ganin dacewar gwamnatin Japan ta bayar da hakuri da sahihiyar zuciya, tare da biyan diyya ga wadanda ta cutar.
Rungumar matsayar masu tsattsauran ra’ayi na Japan daga bangaren mahukunta na jan hankulan al’ummun duniya, inda masu bayyana ra’ayoyin ke ganin hakan zai iya shafar zaman lafiya da tsaron yankinta. Kaso 80.8 bisa dari na ganin jerin abubuwan da suka faru a baya bayan nan daga kalaman mahukuntan Japan, sun yi hannun riga da manufar wanzar da zaman lafiya.
CGTN ta gabatar da kuri’un jin ra’ayin jama’ar ne ta harsunan Turancin Ingilishi, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da harshen Rasha. Inda masu bayyana ra’ayoyi 10,451 suka fayyace mahangarsu cikin sa’o’i 24. (Mai fassara: Saminu Alhassan)














