ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?

by Sulaiman
7 months ago
Sojojin somaliya

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

Juyin mulki, wani lamari ne da ya zama abun mamaki a shekarun baya amma a ‘yan shekarun nan, a iya cewa, ba abun mamaki ba ne domin ya zama tamkar ruwan dare musamman a Nahiyar Afirka. 
Masoynmu masu bibiyarmu, me zai hana, mu tambayi kanmu, shin me ake nufi da juyin mulki kuma me ke kawo shi?
Juyin mulki, shi ne ƙwace gwamnatin ƙasa ba zato ba tsammani kuma ba bisa ƙa’ida ba, wanda yawanci sojoji ko ƙungiya mai ƙarfi ke yi, ta hanyar amfani da ƙarfi ko barazana domin cire zaɓaɓɓun shugabanni.
A wannan makon, alƙalaminmu zai karkata ne kan sharhi ga wannan muhimmin abu da ke barazana ga wanzuwar dimokuraɗiyya a yankin Afirka, duk da cewa, akwai dalilai masu ƙarfi da ke janyo a yi juyin mulki a ƙasa.
Ga bayani a sarari kuma a taƙaice game da manyan dalilan da ake kyautata zaton su suke haifar da juyin mulkin da ake yi kwanan nan a Afirka, musamman daga ƙarshen shekarun 2020 zuwa 2025.
Duk da cewa, kowacce ƙasa da na ta irin sanadin, kamar a ƙasashe irin Mali, Burkina Faso, Guinea, Nijar, Gabon, Chad, da Sudan da suka fada hannun mulkin sojoji a ‘yan shekarun da suka gabata.
Babban dalilin juyin mulki, bai gaza rashin Shugabanci na gari da cin hanci da rashawa. Gwamnatoci da yawa a ƙasashen da abin ya shafa suna fama da cin hanci da rashawa, rashin kula da ababen more rayuwar jama’a, rashin samar da wutar lantarki, ayyukan yi, ilimi, da kiwon lafiya na gari.
Wannan yana raunana amincewar mutane ga gwamnatocin farar hula kuma yana haifar da gurɓacewar mulkin dimokuraɗiyya wanda hakan ke bai wa sojoji uzurin karɓar mulki cikin sauƙi.
Wasu daga cikin dalilan sun haɗa da rashin tsaro da yawaitar tashe-tashen hankula. Ƙasashen Sahel, kamar Mali, Burkina Faso, Nijar – sun fuskanci hare-haren ta’addanci daga ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi (IS, Al-Qaeda, JANIM), wanda hakan ya haifar da zargin cewa, jami’an tsaron ƙasa sun gaza. A duk lokacin da gwamnatoci suka gaza kare ‘yan ƙasa, sojoji sukan amfani da wannan dama wajen ƙwace mulki da nufin “dawo da tsaro.”
Wasu shugabanni, sukan yi yunƙurin yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulki don sauya kujerar dimokuraɗiyya ta zama ta dindindin, kuma su yi riƙa tafka maguɗi a yayin zaɓe, kamar Guinea (2021) da Gabon (2023). Wannan sau da yawa ya kan fusata jama’a sai hakan ya zama wani uzuri ga sojoji wajen hamɓarar da gwamnatin.
Har ila yau, wasu jama’a saboda fusata da salon mulkin dimokuraɗiyya a ƙasarsu, suna ganin sojoji a matsayin masu ceto, sun yi imanin cewa, sojoji za su kawo musu kwanciyar hankali. Wannan amincewar ta jama’a, yana sa juyin mulki ya yi nasara cikin sauƙi.
Jerin juyin mulki da aka yi cikin nasara a Afirka.
1 – Sojojin Mali a 2020 sun tsige Shugaba Ibrahim Boubacar Keïta saboda rashin tsaro da zanga-zanga.
2 – Sojojin Chad a 2021 sun karɓi mulki a ƙarƙashin ɗan Shugaba Idriss Déby, bayan mutuwar sa.
3 – Sojojin Guinea a 2021 sun tsige Alpha Condé a 2021 bayan yunƙurin tsawaita mulkinsa.
4 – Sojojin Sudan sun rushe gwamnatin raba iko a 2021
5 – Sojojin Burkina Faso a 2022 sun tsige Shugaba Kaboré saboda gazawar dakatar da rashin tsaro. A juyin mulki na biyu kuma, wata tawagar sojoji ta hambarar da Laftanar Kanar Damiba duk a wannan shekara.
6 – Sojojin Nijar a 2023 sun hamɓarar da gwamnatin Bazoum.
7 – Sojojin Gabon a 2023 sun hamɓarar da gwamnatin Ali Bongo.
8 – Sojojin Guinea-Bissau a watan Nuwamban 2025, sun hamɓarar da gwamnatin Umar Sissoco Embalò.
Akwai jerin juyin mulki da aka yi yunƙurin aiwatarwa amma bai yi nasara ba da dama duk a nahiyar ta Afirka.
Juyin mulki
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin
  • Sulaiman
    Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa
  • Sulaiman
    Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa
Manyan Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Next Post
Wacce Kasa Ce Za Ta Lashe Gasar Kofin Afirka

Yadda Haaland Ya Zura Kwallaye 100 A Firimiyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.