Kwamitin tsaron MDD ya gudanar da taron tattauna halin da ake ciki a Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo a jiya Jumma’a, inda ya mayar da hankali ga batun tabarbarewar yanayin tsaro a gabashin kasar, da kuma wa’adin aikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake kasar ko MONUSCO a nan gaba.
A gun taron, wakilin Sin ya bukaci kungiyar ’yan tawaye ta Kongo, da ta gaggauta tsagaita bude wuta nan take, yana mai kira da a warware sabani ta hanyar tattaunawa ta gaskiya, da kuma soke takunkumi kan ayyukan MONUSCO, da kuma daidaita wa’adin aikin MONUSCO zuwa lokacin kyautatuwar yanayi a kasar, ta yadda za a tabbatar da amincin MONUSCO da kwamitin tsaron MDD. (Safiyah Ma)
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT














