A yau Asabar ne aka gudanar da taron tunawa da kisan kiyashin birnin Nanjing na kasar Sin karo na 12, domin karrama kusan mutane 300,000 da dakarun mamaya na kasar Japan suka hallaka a garin na Nanjing. A wannan karo, taron ya zo daidai lokacin da ake bikin cika shekaru 80 da kawo karshen yakin duniya na biyu.
Duk da yanayin hunturu da ake ciki, dubban al’ummun birnin Nanjing sanye da bakaken tufafi, sun yi dafifi a dandalin taruwar jama’a na babban zauren tunawa da kisan kiyashin Nanjing, wanda ke lardin Jiangsu na gabashin kasar Sin. Mahalarta taron sun makala fararen furanni a kirji, don shaida wannan biki.
An sassauto da tutar kasar Sin zuwa rabin sanda gaban mahalarta taron, wadanda suka hada da mutanen da suka tsira daga kisan kiyashin, da daliban birnin da ma baki daga sassan kasa da kasa.
Da karfe 10:01 na safiyar dau din, an kunna jiniya mai karar gaske, kana matuka motoci a garin sun dakata, tare da dannan hon din motocinsu a lokaci guda, yayin da matafi a kasa suka tsaitsaya domin yin shiru na dan wani lokaci, a wani mataki na karrama wadanda kisan kiyashin birnin ya rutsa da su.
A ranar 13 ga watan Disamban shekarar 1937 ne dakarun mamaya na kasar Japan suka aikata kisan kare dangi ga al’ummar Nanjing, bayan sun kwace iko da birnin, wanda a lokacin shi ne fadar mulkin kasar Sin.
Cikin makwanni shida, dakarun na Japan sun hallaka Sinawa fararen hula, da sojoji da ba sa dauke da makamai kimanin 300,000, a wata ta’asa mafi muni da ta auku yayin yakin duniya na biyu.
Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS Shi Taifeng, ya halarci taron tare da gabatar da jawabi. Cikin jawabin na sa, ya yi kira ga daukacin Sinawa da su zage-damtse wajen ingiza farfado da kasa, da bayar da gagarumar gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya da ci gaban bil’adama. (Mai fassara: Saminu Alhassan)














