Tsohon jakadan kasar Singapore a Majalisar Dinkin Duniya, Kishore Mahbubani, ya yabawa hangen nesan kasar Sin, da yadda kasar ke la’akari da manyan tsare-tsaren raya kai. Mahbubani ya yi tsokacin ne yayin zantawa da wakilin kafar CMG a kwanan baya.
A cewarsa, yanzu haka kasar Sin tana tsara shirin raya kasa domin shekaru biyar masu zuwa, wanda hakan ya nuna yadda kasar ke iya tsara manyan tsare-tsare na dogon lokaci. Tsohon jakadan ya kara da cewa yayin da wata kasa ke neman samun ci gaba, tana bukatar dogaro kan kasuwa mai ‘yanci, gami da ingantattun manufofin da gwamnati ke dauka, wannan shi ne ke kunshe cikin tunani mai daraja, da salon raya tattalin arziki na kasar Sin.
Ya kara da cewa, ban da mai da hankali kan saurin karuwar tattalin arziki, yanzu haka kasar Sin na dora karin muhimmanci kan ingancin karuwarsa, da kare muhalli, da kyautatuwar rayuwar jama’a. Ta hanyar daukar manufofi masu dacewa, kasar ta cimma nasarar fitar da mutanenta miliyan 800 daga kangin talauci. Ya ce idan sauran kasashe sun yi koyi daga fasahohin kasar Sin na rage talauci, tare da aiwatar da su cikin shekaru 10 zuwa 20 masu zuwa, tabbas rayuwar daukacin bil Adama za ta kyautu sosai.
Sa’an nan, dangane da huldar dake tsakanin kasar Sin da kasar Amurka, Mahbubani ya ce, darajar cinikin da kasar Sin take yi tare da sauran kasashe ta fi ta cinikin da Amurka take yi da su, kana kasashe daban daban na bukatar dimbin kayayyakin da kasar Sin take samarwa wajen raya masana’antunsu. Ta haka ake iya ganin tasirin kasar Sin kan tsarin tattalin arziki na duniya. Saboda haka, idan kasar Amurka ta nemi katse huldar ciniki da Sin, to hakan zai zama tamkar katse huldarta ne da sauran kasashe daban daban.
Kishore Mahbubani ya kara da cewa, ya kamata kasar Amurka ta daina daukar matakan hana kasar Sin ci gaba, sa’an nan ta yi kokarin hadin gwiwa tare da kasar Sin, bisa wani salo da zai amfani dukkan bangarorin 2. (Bello Wang)













