• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fitar Da Sabon Bayani Kan Murar Tsintsaye

by Abubakar Abba
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Bayan tabbatar da barkewar annobar murar tsunitsaye a jihar Legas da Osun da Bayelsa, gwamnatin tarayya ta bukaci masu kiwo a kasar nan, musamman a wadannan jihohin hudu da su daukin matakan da suka kamata domin a dakile yaduwar annobar zuwa sauran guraren da ake yin kiwo a kasar nan.

Kungiyar likitocin dabbobi ce ta gano barkewar annobar a cikin watan Okutobar wannan shekarar.

  • Asirin Namiji Mai Zamba Da Shigar Mata Ya Tonu
  • Jam’iyyar APC A Kano Na So A Hukunta Bashir Ahmad Kan Halartar Gasar Cin Kofin Duniya A Qatar

Wannan bukatar ta gwamnatin na kunshe ne a cikin wata wasika da Dakta Maimuna Abdullahi Habib, Darakta a sashen kula da lafiyar dabbobi da kare yaduwar cutukan da ke harbin dabboni ta ma’aikatar aikin gona da raya karkara ta tarayya ta aike wa da daukin daraktocin hukomomin kula da kiwon lafiyar dabbobi da ke a jihohin kasar nan 36 har da Abuja a makon da ya wuce akan maganar barkewar annobar.

Dakta Maimuna ta sanar da cewa, barkewar cutar a jihohi 29 a watan Janairun shekarar 2021 an dan samu tazara mai tsawon lokaci, inda ta ci gaba da cewa, gwajin da aka yi a kwanan baya, ya tabbatar da sabuwar barkewa cutar da kuma yaduwar ta, a saboda haka, ya zama wajibi a dauki matakan dakile ci gaba da yaduwar ta zuwa sauran guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona a kasar nan.

A cewar Dakta Maimuna, bisa kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi na daukar matakan dakile yaduwar cutar ta samar da wani, tsari na sanya a duba guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona, inda bincike ya nuna cewa, wasu masu kiwon Kajin na gidan gona ba sa bin matakan da ya dace na yin kiwon musamman yadda suke gwamatsa Kajin a wajen daya da kuma rashin yi musu allurar riga-kafi a lokacin da ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

“Ya zama wajibi a dauki matakan dakile ci gaba da yaduwar ta zuwa sauran guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin kasar nan”.

Dakta Maimuna ta ci gaba da cewa, sauran matsalolin da aka gano sun hada da, rashin kula da Kajin da wasu masu kiwata su ba sa yi yadda ya dace wajen hada Kajin da sauran tsitsayen da suke kiwata wa duk a waje daya, jinkirin da ake samu wajen fitar da sakamakon gwajin Kajin na gidan gona da ake gani ba su da lafiya, jigilar kwan Kajin da masu hada-hadar kasuwancinsa ke yi a cikin mota daga arewacin Nijeriya zuwa kudancin kasar nan.

“Ina kira ga masu kiwon da sauran masu ruwa da tsaki a fannin da su guje wa yin kiwon ba bisa ka’ida ba domin a gujewa tada cutar zuwa ga sauran gidajen gona da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin Nijeriya”.

Daraktar ta yi kira ga masu kiwon da sauran masu ruwa da tsaki a fannin da su gujewa yin kiwon ba bisa ka’ida ba domin a gujewa tada cutar zuwa ga sauran gidajen gona da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.