• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fitar Da Sabon Bayani Kan Murar Tsintsaye

by Abubakar Abba
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Bayan tabbatar da barkewar annobar murar tsunitsaye a jihar Legas da Osun da Bayelsa, gwamnatin tarayya ta bukaci masu kiwo a kasar nan, musamman a wadannan jihohin hudu da su daukin matakan da suka kamata domin a dakile yaduwar annobar zuwa sauran guraren da ake yin kiwo a kasar nan.

Kungiyar likitocin dabbobi ce ta gano barkewar annobar a cikin watan Okutobar wannan shekarar.

  • Asirin Namiji Mai Zamba Da Shigar Mata Ya Tonu
  • Jam’iyyar APC A Kano Na So A Hukunta Bashir Ahmad Kan Halartar Gasar Cin Kofin Duniya A Qatar

Wannan bukatar ta gwamnatin na kunshe ne a cikin wata wasika da Dakta Maimuna Abdullahi Habib, Darakta a sashen kula da lafiyar dabbobi da kare yaduwar cutukan da ke harbin dabboni ta ma’aikatar aikin gona da raya karkara ta tarayya ta aike wa da daukin daraktocin hukomomin kula da kiwon lafiyar dabbobi da ke a jihohin kasar nan 36 har da Abuja a makon da ya wuce akan maganar barkewar annobar.

Dakta Maimuna ta sanar da cewa, barkewar cutar a jihohi 29 a watan Janairun shekarar 2021 an dan samu tazara mai tsawon lokaci, inda ta ci gaba da cewa, gwajin da aka yi a kwanan baya, ya tabbatar da sabuwar barkewa cutar da kuma yaduwar ta, a saboda haka, ya zama wajibi a dauki matakan dakile ci gaba da yaduwar ta zuwa sauran guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona a kasar nan.

A cewar Dakta Maimuna, bisa kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi na daukar matakan dakile yaduwar cutar ta samar da wani, tsari na sanya a duba guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona, inda bincike ya nuna cewa, wasu masu kiwon Kajin na gidan gona ba sa bin matakan da ya dace na yin kiwon musamman yadda suke gwamatsa Kajin a wajen daya da kuma rashin yi musu allurar riga-kafi a lokacin da ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

“Ya zama wajibi a dauki matakan dakile ci gaba da yaduwar ta zuwa sauran guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin kasar nan”.

Dakta Maimuna ta ci gaba da cewa, sauran matsalolin da aka gano sun hada da, rashin kula da Kajin da wasu masu kiwata su ba sa yi yadda ya dace wajen hada Kajin da sauran tsitsayen da suke kiwata wa duk a waje daya, jinkirin da ake samu wajen fitar da sakamakon gwajin Kajin na gidan gona da ake gani ba su da lafiya, jigilar kwan Kajin da masu hada-hadar kasuwancinsa ke yi a cikin mota daga arewacin Nijeriya zuwa kudancin kasar nan.

“Ina kira ga masu kiwon da sauran masu ruwa da tsaki a fannin da su guje wa yin kiwon ba bisa ka’ida ba domin a gujewa tada cutar zuwa ga sauran gidajen gona da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin Nijeriya”.

Daraktar ta yi kira ga masu kiwon da sauran masu ruwa da tsaki a fannin da su gujewa yin kiwon ba bisa ka’ida ba domin a gujewa tada cutar zuwa ga sauran gidajen gona da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.