• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fitar Da Sabon Bayani Kan Murar Tsintsaye

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya Ta Fitar Da Sabon Bayani Kan Murar Tsintsaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan tabbatar da barkewar annobar murar tsunitsaye a jihar Legas da Osun da Bayelsa, gwamnatin tarayya ta bukaci masu kiwo a kasar nan, musamman a wadannan jihohin hudu da su daukin matakan da suka kamata domin a dakile yaduwar annobar zuwa sauran guraren da ake yin kiwo a kasar nan.

Kungiyar likitocin dabbobi ce ta gano barkewar annobar a cikin watan Okutobar wannan shekarar.

  • Asirin Namiji Mai Zamba Da Shigar Mata Ya Tonu
  • Jam’iyyar APC A Kano Na So A Hukunta Bashir Ahmad Kan Halartar Gasar Cin Kofin Duniya A Qatar

Wannan bukatar ta gwamnatin na kunshe ne a cikin wata wasika da Dakta Maimuna Abdullahi Habib, Darakta a sashen kula da lafiyar dabbobi da kare yaduwar cutukan da ke harbin dabboni ta ma’aikatar aikin gona da raya karkara ta tarayya ta aike wa da daukin daraktocin hukomomin kula da kiwon lafiyar dabbobi da ke a jihohin kasar nan 36 har da Abuja a makon da ya wuce akan maganar barkewar annobar.

Dakta Maimuna ta sanar da cewa, barkewar cutar a jihohi 29 a watan Janairun shekarar 2021 an dan samu tazara mai tsawon lokaci, inda ta ci gaba da cewa, gwajin da aka yi a kwanan baya, ya tabbatar da sabuwar barkewa cutar da kuma yaduwar ta, a saboda haka, ya zama wajibi a dauki matakan dakile ci gaba da yaduwar ta zuwa sauran guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona a kasar nan.

A cewar Dakta Maimuna, bisa kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi na daukar matakan dakile yaduwar cutar ta samar da wani, tsari na sanya a duba guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona, inda bincike ya nuna cewa, wasu masu kiwon Kajin na gidan gona ba sa bin matakan da ya dace na yin kiwon musamman yadda suke gwamatsa Kajin a wajen daya da kuma rashin yi musu allurar riga-kafi a lokacin da ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

“Ya zama wajibi a dauki matakan dakile ci gaba da yaduwar ta zuwa sauran guraren da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin kasar nan”.

Dakta Maimuna ta ci gaba da cewa, sauran matsalolin da aka gano sun hada da, rashin kula da Kajin da wasu masu kiwata su ba sa yi yadda ya dace wajen hada Kajin da sauran tsitsayen da suke kiwata wa duk a waje daya, jinkirin da ake samu wajen fitar da sakamakon gwajin Kajin na gidan gona da ake gani ba su da lafiya, jigilar kwan Kajin da masu hada-hadar kasuwancinsa ke yi a cikin mota daga arewacin Nijeriya zuwa kudancin kasar nan.

“Ina kira ga masu kiwon da sauran masu ruwa da tsaki a fannin da su guje wa yin kiwon ba bisa ka’ida ba domin a gujewa tada cutar zuwa ga sauran gidajen gona da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin Nijeriya”.

Daraktar ta yi kira ga masu kiwon da sauran masu ruwa da tsaki a fannin da su gujewa yin kiwon ba bisa ka’ida ba domin a gujewa tada cutar zuwa ga sauran gidajen gona da ake kiwata Kajin na gidan gona a daukacin fadin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaMurar Tsuntsaye
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Next Post

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

6 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

6 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

6 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.