• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Tir Da Yadda Gwamnatin Zamfara Ke Siyasantar da Matsalar Tsaro

by Sulaiman
2 years ago
Gwamnatin tarayya

Gwamnatin Tarayya ta bayyana matuƙar damuwa kan wata sanarwa da ta fito daga Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Dauda Lawal Dare.

Gwamnatin ta ce maimakon gwamnan ya nuna jin daɗi da farin ciki ganin yadda jami’an tsaro da hukumomin Gwamnatin Tarayya ke ta ƙoƙarin ganin an ceto ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Gusau daga hannun ‘yan bindiga, sai ya maida matsalar siyasa don kawai ya cimma wani buri a siyasance.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Zargin Tattaunawa Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Bukukuwan Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Ranar Haihuwar Fiyayyen Halitta.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka bayan ya nazarci yadda dokar ƙasa ta bai wa hukumomin Gwamnatin Tarayya ƙarfin ikon zabura domin ɗaukar matakan tabbatar da ceto waɗanda aka yi garkuwa da su, kamar irin yadda aka yi wa ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Gusau.

A cewar sa, don hukumomin da aikin ceton ɗaliban ba su fito sun sanar da irin ayyukan ceto ɗaliban ba, hakan ba ya nufin ana wata ƙumbiya-ƙumbiya kamar yadda gwamnan Zamfara ya yi wa ƙoƙarin da ake yi karkatacciyar fahimta.

A wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai a Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Suleiman Haruna, ya rattaba wa hannu, ministan ya bayyana cewa babu wani jami’in Gwamnatin Tarayya wanda ke tattaunawar sulhu da wani ko wasu gungun ‘yan bindiga.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Ya ce ita Gwamnatin Tarayya ta na nan kan matsayar ta ta tabbatar da bin duk wasu hanyoyin da su ka dace, waɗanda binsu zai tabbatar da an daƙile tashin hankula kuma an dawo da zaman lafiya a cikin jama’a.

Sai dai kuma ya ce, idan jama’ar wasu yankuna su ka yi tunanin ɗaukar irin matakan da wasu yankuna su ka ɗauka har su ka kashe fitilar tashe-tashen hankula, ta hanyar neman sasantawa, to Gwamnatin Tarayya ba za ta yi gaggawar taka masu burki ko yi wa shirin nasu Allah-wadai ba.

Idris ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa Gwamnatin Tarayya da sauran hukumomin ta na aiki haiƙan don kawo ƙarshen matsalar ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da duk wasu ayyukan laifuffuka.

Daga ƙarshe, ministan ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta saurari shawarwarin dukkan masu wani tasiri domin ƙoƙarin samun hanyoyin da za a bi a kawo ƙarshen matsalolin tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Manchester City

Newcastle Ta Kori Manchester City A Gasar League Cup Ta Kasar Ingila

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.