ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Tir Da Yadda Gwamnatin Zamfara Ke Siyasantar da Matsalar Tsaro

by Sulaiman
3 years ago
Gwamnatin tarayya

Gwamnatin Tarayya ta bayyana matuƙar damuwa kan wata sanarwa da ta fito daga Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Dauda Lawal Dare.

Gwamnatin ta ce maimakon gwamnan ya nuna jin daɗi da farin ciki ganin yadda jami’an tsaro da hukumomin Gwamnatin Tarayya ke ta ƙoƙarin ganin an ceto ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Gusau daga hannun ‘yan bindiga, sai ya maida matsalar siyasa don kawai ya cimma wani buri a siyasance.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Zargin Tattaunawa Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Bukukuwan Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Ranar Haihuwar Fiyayyen Halitta.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka bayan ya nazarci yadda dokar ƙasa ta bai wa hukumomin Gwamnatin Tarayya ƙarfin ikon zabura domin ɗaukar matakan tabbatar da ceto waɗanda aka yi garkuwa da su, kamar irin yadda aka yi wa ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Gusau.

ADVERTISEMENT

A cewar sa, don hukumomin da aikin ceton ɗaliban ba su fito sun sanar da irin ayyukan ceto ɗaliban ba, hakan ba ya nufin ana wata ƙumbiya-ƙumbiya kamar yadda gwamnan Zamfara ya yi wa ƙoƙarin da ake yi karkatacciyar fahimta.

A wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai a Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Suleiman Haruna, ya rattaba wa hannu, ministan ya bayyana cewa babu wani jami’in Gwamnatin Tarayya wanda ke tattaunawar sulhu da wani ko wasu gungun ‘yan bindiga.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Ya ce ita Gwamnatin Tarayya ta na nan kan matsayar ta ta tabbatar da bin duk wasu hanyoyin da su ka dace, waɗanda binsu zai tabbatar da an daƙile tashin hankula kuma an dawo da zaman lafiya a cikin jama’a.

Sai dai kuma ya ce, idan jama’ar wasu yankuna su ka yi tunanin ɗaukar irin matakan da wasu yankuna su ka ɗauka har su ka kashe fitilar tashe-tashen hankula, ta hanyar neman sasantawa, to Gwamnatin Tarayya ba za ta yi gaggawar taka masu burki ko yi wa shirin nasu Allah-wadai ba.

Idris ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa Gwamnatin Tarayya da sauran hukumomin ta na aiki haiƙan don kawo ƙarshen matsalar ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da duk wasu ayyukan laifuffuka.

Daga ƙarshe, ministan ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta saurari shawarwarin dukkan masu wani tasiri domin ƙoƙarin samun hanyoyin da za a bi a kawo ƙarshen matsalolin tsaro.

Matsalar tsaro
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna
  • Sulaiman
    Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar
  • Sulaiman
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna
Labarai

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
Manyan Labarai

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Next Post
Manchester City

Newcastle Ta Kori Manchester City A Gasar League Cup Ta Kasar Ingila

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.