Gwamnatin Sin ta aika da zagayen farko na kayayyakin agajin gaggawa ga Venezuela, domin tallafa wa ayyukan jin kai sanadiyyar aukuwar girgizar kasa. Wadannan kayayyaki sun tashi daga filin jirgin sama na kasa da kasa na Beijing a daren jiya 5 ga watan Yuli.
An bayyana cewa, wadannan kayayyaki sun hada da injinan samar da wuta 20 da motocin tsabtace ruwa 8 da injunan kashe kwayoyin cuta 200, kana da na’urorin hasken rana 200 da tantuna 1,700, da barguna 6,700. An yi jigilar su ne da jirgin sama na musamman zuwa babban birnin Venezuela Caracas. Za kuma a ci gaba da aika sauran kayayyakin jin kai.
A ranar 24 ga watan Yuni ne aka yi girgizar kasa mai karfi a Venezuela, wadda ta haddasa asarar rayuka da dukiya mai yawa. Adadin wadanda suka mutu ya haura zuwa 3,342, yayin da 16,740 suka jikkata. Bayan girgizar, gwamnatin Sin ta tura kudaden agaji na gaggawa ga Venezuela. (Amina Xu)














