Aƙalla mutane 15 ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a yankin Makabartar Musulmi da ke kan titin Ogbomoso–Oko Olowo a babban titin Ilorin–Jebba, a Jihar Kwara.
Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) na Jihar Kwara, Kabir Kazeem, ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a ranar Litinin a Ilorin.
Kazeem ya ce hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:32 na dare, inda wata babbar mota kirar DAF XF mai lambar rajista GWL 274 XC ta yi hatsari ita kaɗai.
Ya ƙara da cewa mutane maza 48 ne ke cikin motar a lokacin da hatsarin ya faru. Daga cikinsu, mutane 15 sun rasu, 17 sun samu raunuka daban-daban, yayin da wasu 16 suka tsira ba tare da sun ji rauni ba.














