Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gaza magance matsalar yunwa da ke ƙara ƙamari a Nijeriya.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran Jam’iyyar na Ƙasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta ce sama da ‘yan Nijeriya miliyan 17 na fama da matsanancin ƙarancin abinci sakamakon gazawar gwamnati wajen magance rashin tsaro, kare manoma da kuma rage tsadar kayan abinci.
ADC ta yi wannan martani ne bayan rahoton Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana cewa mutane sama da miliyan 17 a jihohi tara da rikici yake shafa a Arewacin Nijeriya na fuskantar matsananciyar yunwa.
Rahoton ya kuma nuna cewa sama da mutane miliyan uku a Jihar Borno na cikin halin yunwa, yayin da adadin mutanen da abin ya shafa a jihohin Borno, Adamawa da Yobe ya kai miliyan 6.2.
Jam’iyyar ta ce rahoton ya tabbatar da cewa rashin tsaro, hare-haren da ake kai wa manoma, da raba al’umma da muhallansu ne suka haddasa ƙarancin abinci, ba wai iftila’in sauyin yanayi ba.
Har ila yau, ADC ta soki gwamnatin Tinubu kan ci gaba da cewa matsin tattalin arziƙin da ake fuskanta na wucin gadi ne, tana mai cewa hauhawar farashin kayan abinci da kom bayan noma na ci gaba da ƙara jefa rayuwar al’umma cikin yunwa.
Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa idan ta samu damar hawan kan mulki, za ta bai wa harkar samar da abinci muhimmanci ta hanyar tallafa wa manoma, bunƙasa noma, da kuma samar da ingantattun wuraren adana amfanin gona domin rage asara da daidaita farashin kayan abinci.
A ƙarshe, ADC ta yi kira ga gwamnati da ta ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalar yunwa da rashin tsaro da ke addabar ƙasar.













