ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

by Sadiq
3 weeks ago

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gaza magance matsalar yunwa da ke ƙara ƙamari a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran Jam’iyyar na Ƙasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta ce sama da ‘yan Nijeriya miliyan 17 na fama da matsanancin ƙarancin abinci sakamakon gazawar gwamnati wajen magance rashin tsaro, kare manoma da kuma rage tsadar kayan abinci.

ADC ta yi wannan martani ne bayan rahoton Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana cewa mutane sama da miliyan 17 a jihohi tara da rikici yake shafa a Arewacin Nijeriya na fuskantar matsananciyar yunwa.

ADVERTISEMENT

Rahoton ya kuma nuna cewa sama da mutane miliyan uku a Jihar Borno na cikin halin yunwa, yayin da adadin mutanen da abin ya shafa a jihohin Borno, Adamawa da Yobe ya kai miliyan 6.2.

Jam’iyyar ta ce rahoton ya tabbatar da cewa rashin tsaro, hare-haren da ake kai wa manoma, da raba al’umma da muhallansu ne suka haddasa ƙarancin abinci, ba wai iftila’in sauyin yanayi ba.

LABARAI MASU NASABA

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Har ila yau, ADC ta soki gwamnatin Tinubu kan ci gaba da cewa matsin tattalin arziƙin da ake fuskanta na wucin gadi ne, tana mai cewa hauhawar farashin kayan abinci da kom bayan noma na ci gaba da ƙara jefa rayuwar al’umma cikin yunwa.

Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa idan ta samu damar hawan kan mulki, za ta bai wa harkar samar da abinci muhimmanci ta hanyar tallafa wa manoma, bunƙasa noma, da kuma samar da ingantattun wuraren adana amfanin gona domin rage asara da daidaita farashin kayan abinci.

A ƙarshe, ADC ta yi kira ga gwamnati da ta ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalar yunwa da rashin tsaro da ke addabar ƙasar.

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Next Post
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

LABARAI MASU NASABA

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.