Rahotanni sun bayyana cewa dakarun Rundunar Juyin Juya Halin Iran (IRGC) sun harba aƙalla makamai masu linzami biyu kan wasu jiragen ruwan kasuwanci da ke ratsawa ta Mashigar Hormuz.
Kafar yaɗa labarai ta Axios, ta ce an kai harin ne a daren ranar Litinin, inda wasu jiragen ruwa biyu suka lalace, sai dai babu rahoton asarar rai.
Hukumar Kula da Harkokin Jiragen Ruwa ta Birtaniya (UKMTO) ta tabbatar da cewa an kai wa wani jirgin dakon mai hari a kusa da yankin Limah da ke ƙasar Oman.
Hukumar ta ce harin ya haddasa gobara a jirgin, amma babu wanda ya mutu.
Rahotanni sun ce ɗaya daga cikin jiragen da aka kai wa hari shi ne Al Rekayyat, wani jirgin dakon gas da kamfanin Nakilat na Qatar ke amfani da shi.
An ce makamin ya faɗa kusa da sashen injin jirgin, lamarin da ya janyo tashin wuta da hayaƙi.
Jaridar Wall Street Journal ta ce duk da harin, ma’aikatan jirgin sun tsira kuma an kai su waje mai aminci a cikin jirgin.
Lamarin na zuwa ne bayan tattaunawar da Amurka da Iran suka yi a makon da ya gabata ba ta kai ga cimma wata sabuwar yarjejeniyar zaman lafiya ba, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da ake fatan za ta rage tashin hankali tsakanin ɓangarorin.
A ranar Litinin, Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa Amurka za ta cimma yarjejeniya da Iran ko kuma ta ɗauki wasu matakai idan hakan ya gagara.
Masana sun ce rikicin na ci gaba da jefa fargaba a kasuwannin duniya, musamman kan zirga-zirgar jiragen ruwa da kuma safarar ɗanyen mai ta Mashigar Hormuz, wadda ke daga cikin manyan hanyoyin jigilar mai a duniya.













