Hukumar kwallon ta nahiyar Turai (UEFA) ta soki matakin da hukumar kwallon kasa ta Duniya (FIFA) ta dauka na dakatar da aiwatar da haramcin wasa daya ga dan wasan gaban tawagar kasar Amurka Folarin Balogun, tana mai bayyana matakin a matsayin wanda ya “keta ka’ida” kuma tayi gargadin cewa zai iya taba mutuncin hukumar kwallon kafar.
A cikin wata sanarwa, hukumar kwallon kafa ta Turai ta ce soke hukuncin dakatarwar ya saba wa daya daga cikin muhimman ka’idojin wasan, “Shawarar da aka yanke jiya na soke dakatarwar wasa daya bayan jan katin da aka bai wa Folarin Balogun ya saba kaidar kwallon kafa,” in ji UEFA.
Hukumar ta kara da cewa duk da cewa akwai wasu kaidojin kwallon kafa da ke bukatar sake dubawa, amma kuma dakatarwa bayan samun katin kora baya cikinsu.
A cewar UEFA, haramcin wasa daya yana cikin manyan dokokin kwallo don haka “ba za a iya keta shi ba,” musamman a lokacin gasar cin kofin Duniya da ake ci gaba da yi, inda zuwa yanzu an riga an dakatar da wasu yan wasan kuma ta tabbata, UEFA ta yi gargadin cewa rashin aiwatar da dokokin yana barazana ga ingancin wasan da kuma ingancin gasar.
Ta kuma yi gargadin cewa hukuncin na iya janyo wani ya sake neman yafiya idan ya aikata kwatankwacin wannan laifin a gaba, a halin yanzu tsohon shugaban FIFA Sepp Blatter shima ya nuna damuwa dangane da hukuncin na FIFA, yana mai cewa ana some katin kora ta hanyar doka ba ta hanyar kiran waya daga wani ba, ya kara da cewa “Kwallon kafa ba za ta taba zama filin wasan yan siyasa ba.”














