ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

by Sadiq
1 hour ago

Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Kano, ta tilasta wa wani Alƙalin Kotu yin ritaya bayan samun sa da laifin karɓar cin hanci.

Haka kuma, ta ɗauki matakan ladabtarwa kan wasu alƙalai da ma’aikatan kotu bisa laifukan rashin ɗa’a.

Matakin ya biyo bayan taron hukumar karo na 90 da aka gudanar a ranar 3 ga watan Yuli, bayan nazarin rahotannin Kwamitin Karɓar Ƙorafe-ƙorafen Jama’a kan ma’aikatan shari’a.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da kakakin Kotunan Jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim, ya fitar, ya ce an ɗauki matakan ne domin kare mutuncin harkar shari’a da inganta amincewar jama’a da kotuna.

Hukumar ta umarci Alƙali Aliyu Yahaya Muhammad na Kotun Shari’a ta Bebeji da ya yi ritaya nan take bayan bincike ya tabbatar da cewa ya karɓi cin hancin Naira 250,000 yayin gudanar da wata shari’a.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Haka kuma, an umarce shi da ya mayar da kuɗin.

Sai kuma magatakardar kotun, Ibrahim Ahmad Ibrahim, wanda aka dakatar da shi na tsawon watanni huɗu ba tare da albashi ba, bayan ya amsa cewa ya karɓi wani ɓangare na kuɗin cin hancin.

Har ila yau, hukumar ta tilasta wa Muzambilu Ado, muƙaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Kano, yin ritaya saboda kura-kurai da aka gano a takardun karatunsa da kuma yadda aka ɗauke shi aiki.

Haka kuma, an rage wa Alƙali Usman Haruna Usman na Babbar Kotun Shari’a ta Goron Dutse matsayi saboda sakaci da ya sa aka tura kuɗin da aka samu daga sayar da kadarorin da kotu ta ƙwace zuwa asusun wani ma’aikacin kotu.

Alƙali Abdullahi Wayya na Kotun Kasuwa kuwa gargaɗi aka yi masa saboda sakaci wajen sa ido kan bayar da beli, lamarin da ya sa aka saki wanda ake tuhuma ba tare da cikakken tantance takardun belin ba.

Hukumar ta kuma umarci Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta binciki Sufeto Shehu Adamu bisa zargin yaudarar kotu, tare da ba da umarnin binciken wasu ma’aikatan kotu biyu kan rawar da suka taka wajen bayar da takardun belin.

Hakazalika, hukumar ta janye dakatarwar da ta yi wa Alƙali Umar Sunusi Danbaba bayan sake nazarin wasu sabbin takardu.

Ta kuma mayar masa da albashi da sauran haƙƙoƙinsa tare da umartar sa ya koma bakin aiki.

A ƙarshe, Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Kano ta sake jaddada aniyarta na tabbatar da gaskiya da riƙon amana a harkar shari’a, tana mai gargaɗin cewa duk wani ma’aikacin shari’a da aka samu da laifin cin hanci ko rashin ɗa’a zai fuskanci hukuncin da ya dace da shi.

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026

LABARAI MASU NASABA

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.