ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

by Sadiq
3 weeks ago

Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Kano, ta tilasta wa wani Alƙalin Kotu yin ritaya bayan samun sa da laifin karɓar cin hanci.

Haka kuma, ta ɗauki matakan ladabtarwa kan wasu alƙalai da ma’aikatan kotu bisa laifukan rashin ɗa’a.

Matakin ya biyo bayan taron hukumar karo na 90 da aka gudanar a ranar 3 ga watan Yuli, bayan nazarin rahotannin Kwamitin Karɓar Ƙorafe-ƙorafen Jama’a kan ma’aikatan shari’a.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da kakakin Kotunan Jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim, ya fitar, ya ce an ɗauki matakan ne domin kare mutuncin harkar shari’a da inganta amincewar jama’a da kotuna.

Hukumar ta umarci Alƙali Aliyu Yahaya Muhammad na Kotun Shari’a ta Bebeji da ya yi ritaya nan take bayan bincike ya tabbatar da cewa ya karɓi cin hancin Naira 250,000 yayin gudanar da wata shari’a.

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

Haka kuma, an umarce shi da ya mayar da kuɗin.

Sai kuma magatakardar kotun, Ibrahim Ahmad Ibrahim, wanda aka dakatar da shi na tsawon watanni huɗu ba tare da albashi ba, bayan ya amsa cewa ya karɓi wani ɓangare na kuɗin cin hancin.

Har ila yau, hukumar ta tilasta wa Muzambilu Ado, muƙaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Kano, yin ritaya saboda kura-kurai da aka gano a takardun karatunsa da kuma yadda aka ɗauke shi aiki.

Haka kuma, an rage wa Alƙali Usman Haruna Usman na Babbar Kotun Shari’a ta Goron Dutse matsayi saboda sakaci da ya sa aka tura kuɗin da aka samu daga sayar da kadarorin da kotu ta ƙwace zuwa asusun wani ma’aikacin kotu.

Alƙali Abdullahi Wayya na Kotun Kasuwa kuwa gargaɗi aka yi masa saboda sakaci wajen sa ido kan bayar da beli, lamarin da ya sa aka saki wanda ake tuhuma ba tare da cikakken tantance takardun belin ba.

Hukumar ta kuma umarci Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta binciki Sufeto Shehu Adamu bisa zargin yaudarar kotu, tare da ba da umarnin binciken wasu ma’aikatan kotu biyu kan rawar da suka taka wajen bayar da takardun belin.

Hakazalika, hukumar ta janye dakatarwar da ta yi wa Alƙali Umar Sunusi Danbaba bayan sake nazarin wasu sabbin takardu.

Ta kuma mayar masa da albashi da sauran haƙƙoƙinsa tare da umartar sa ya koma bakin aiki.

A ƙarshe, Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Kano ta sake jaddada aniyarta na tabbatar da gaskiya da riƙon amana a harkar shari’a, tana mai gargaɗin cewa duk wani ma’aikacin shari’a da aka samu da laifin cin hanci ko rashin ɗa’a zai fuskanci hukuncin da ya dace da shi.

MASU ALAKA

Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Labarai

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano
Labarai

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
Next Post
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.