Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Kano, ta tilasta wa wani Alƙalin Kotu yin ritaya bayan samun sa da laifin karɓar cin hanci.
Haka kuma, ta ɗauki matakan ladabtarwa kan wasu alƙalai da ma’aikatan kotu bisa laifukan rashin ɗa’a.
Matakin ya biyo bayan taron hukumar karo na 90 da aka gudanar a ranar 3 ga watan Yuli, bayan nazarin rahotannin Kwamitin Karɓar Ƙorafe-ƙorafen Jama’a kan ma’aikatan shari’a.
A cikin wata sanarwa da kakakin Kotunan Jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim, ya fitar, ya ce an ɗauki matakan ne domin kare mutuncin harkar shari’a da inganta amincewar jama’a da kotuna.
Hukumar ta umarci Alƙali Aliyu Yahaya Muhammad na Kotun Shari’a ta Bebeji da ya yi ritaya nan take bayan bincike ya tabbatar da cewa ya karɓi cin hancin Naira 250,000 yayin gudanar da wata shari’a.
Haka kuma, an umarce shi da ya mayar da kuɗin.
Sai kuma magatakardar kotun, Ibrahim Ahmad Ibrahim, wanda aka dakatar da shi na tsawon watanni huɗu ba tare da albashi ba, bayan ya amsa cewa ya karɓi wani ɓangare na kuɗin cin hancin.
Har ila yau, hukumar ta tilasta wa Muzambilu Ado, muƙaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Kano, yin ritaya saboda kura-kurai da aka gano a takardun karatunsa da kuma yadda aka ɗauke shi aiki.
Haka kuma, an rage wa Alƙali Usman Haruna Usman na Babbar Kotun Shari’a ta Goron Dutse matsayi saboda sakaci da ya sa aka tura kuɗin da aka samu daga sayar da kadarorin da kotu ta ƙwace zuwa asusun wani ma’aikacin kotu.
Alƙali Abdullahi Wayya na Kotun Kasuwa kuwa gargaɗi aka yi masa saboda sakaci wajen sa ido kan bayar da beli, lamarin da ya sa aka saki wanda ake tuhuma ba tare da cikakken tantance takardun belin ba.
Hukumar ta kuma umarci Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta binciki Sufeto Shehu Adamu bisa zargin yaudarar kotu, tare da ba da umarnin binciken wasu ma’aikatan kotu biyu kan rawar da suka taka wajen bayar da takardun belin.
Hakazalika, hukumar ta janye dakatarwar da ta yi wa Alƙali Umar Sunusi Danbaba bayan sake nazarin wasu sabbin takardu.
Ta kuma mayar masa da albashi da sauran haƙƙoƙinsa tare da umartar sa ya koma bakin aiki.
A ƙarshe, Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Kano ta sake jaddada aniyarta na tabbatar da gaskiya da riƙon amana a harkar shari’a, tana mai gargaɗin cewa duk wani ma’aikacin shari’a da aka samu da laifin cin hanci ko rashin ɗa’a zai fuskanci hukuncin da ya dace da shi.













