Hukumar Kwastam ta Nijeriya, a ranar Litinin, ta ce ta kama wata kwantena cike da makamai da alburusai da aka shigo da su kasar daga kasar Amurka. Kwantenar makaman ta nufi yankin Kudu maso Gabashin Nijeriya ne.
Da yake jawabi a Legas, mukaddashin Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Adewale Adeniyi, ya ce an kama kwantenar ne a tashar jiragen ruwa ta Tin-Can da ke Legas.
Shehun Borno Ya Bukaci Jama’ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa
A cewar Adeniyi, an gano kwantenar makaman ne a yayin wani binciken hadin guiwa tsakanin rundunar ‘yansandan Nijeriya (NPF) da jami’an tsaron farin kaya (DSS) da kuma hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA).
Mukaddashin Hukumar Kwastam, ya bayyana cewa an kama wasu jami’an da ke aiki kan tantance halarcin kayayyakin da aiki shigo wa da su kasa na tashar kan badakalar wannan kwantenar mai dauke da muggan makamai.