Jagoran majalisar shugabancin kasar Libya Mohammed Al-Menfi, ya bayyana jiya Asabar 13 ga watan nan a birnin Tarablus cewa, kasarsa na mayar da hankali sosai ga bunkasa alaka da kasar Sin, tana kuma fatan karfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin a bangarori daban-daban, a wani kokari na kara ingiza dangantakarsu zuwa sabon matsayi.
Mohammed Al-Menfi, ya bayyana hakan ne yayin da sabon jakadan kasar Sin a Libya Ma Xuliang, ya gabatar masa da takardar kama aiki, inda Menfi ya yi maraba da zuwan sabon jakadan na Sin, tare da nuna cewa, akwai dadadden zumunci tsakanin kasashen biyu, kuma hadin gwiwarsu a bangarori daban-daban na da makoma mai haske.
Shi kuwa a nasa bangaren, jakada Ma Xuliang cewa ya yi karkashin jagorancin shugabannin Sin da Libya, bisa manyan tsare-tsare, zai yi kokari tare da Libya, don fadada hadin gwiwar kasashen biyu, da sa kaimi ga ci gaban dangantakar abotarsu bisa manyan tsare-tsare ta hanyar da ta dace. (Murtala Zhang)















Discussion about this post