Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ƙwato dazukan jihar daga hannun masu laifi, yana mai cewa ‘yan ta’adda, da ‘yan bindiga da sauran miyagu ba za su samu mafaka a jihar Kogi ba.
Ododo ya bayyana hakan ne yayin ziyarar da ya kai sansanin horar da sabbin jami’an Forest Guard, inda ya ce manyan dazukan jihar da ba a cika zama a cikinsu ba sun zama ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen tsaro, saboda masu laifi na amfani da su a matsayin maɓoyarsu.
Ya ce ɗaukar aiki da horas da jami’an Forest Guard na daga cikin sabuwar dabarar tsaron jihar domin ƙarfafa sintiri, da hana masu laifi mafaka da kuma taimakawa jami’an tsaro wajen mayar da martani cikin gaggawa. Haka kuma ya yaba wa Bola Ahmed Tinubu da Nuhu Ribadu bisa goyon bayan da suke bayarwa ga shirin.
Gwamnan ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da zuba jari a ɓangaren tsaro ta fuskar kayan aiki, da ƙarin jami’ai da tattara bayanan sirri domin tabbatar da zaman lafiya a faɗin jihar Kogi.















Discussion about this post