JAMB ta sanya ranar 11 ga Mayu, 2026 domin gudanar da taronta na shekara-shekara kan tsarin ɗaukar ɗalibai, inda za a yanke muhimman shawarwari ciki har da mafi ƙarancin makin shiga manyan makarantu na shekarar 2026.
Mai ba hukumar shawara kan hulɗa da jama’a, Fabian Benjamin, ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X (tsohon Twitter) ranar Lahadi.
Taron mai muhimmanci, wanda za a gudanar a Abuja, zai haɗa manyan masu ruwa da tsaki daga ɓangaren manyan makarantu domin tattauna ƙa’idoji da tsara tsarin ɗaukar ɗalibai na zangon karatu na 2026/2027.
ADVERTISEMENT















Discussion about this post