Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bar Abuja zuwa France, inda ya fara wata ziyarar aiki ta ƙasashe uku wadda za ta hada da Kenya da kuma Rwanda.
Jirgin shugaban ƙasar ya tashi daga ɓangaren shugaban ƙasa na filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe a yau Lahadi, a wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa hulɗa ta tattalin arziƙi da jawo jarin ƙasashen waje.
A cewar fadar shugaban ƙasa, Tinubu zai fara da ziyara a Faransa kafin ya wuce Nairobi domin halartar taron Africa–France Summit da za a gudanar daga ranar 11 zuwa 12 ga Mayu, ƙarƙashin jagorancin Emmanuel Macron da kuma William Ruto.
Ana sa ran shugaban ƙasar zai gana da shugabannin duniya da masu zuba jari a wajen taron, domin ƙara ƙarfafa alaƙar tattalin arziƙi ta Nijeriya da ƙasashen duniya, tare da mai da hankali kan sauyin makamashi, da sauyin yanayi, da fasahar zamani da haɗin gwuiwar tattalin arziƙi.
Daga nan kuma, zai wuce Kigali na Rwanda domin halartar taron Africa CEO Forum daga ranar 14 zuwa 15 ga Mayu, inda manyan ‘yan kasuwa da masu tsara manufofi za su tattauna hanyoyin bunƙasa zuba jari da haɓaka tattalin arziƙin Afirka.















Discussion about this post