ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

by Sulaiman and Shehu Yahaya
3 weeks ago
Malama

Wani mummunan al’amari da ya girgiza zukatan al’umma ya faru a yankin Maraban Jos da ke ƙaramar hukumar Igabi a Jihar Kaduna, inda wata malamar Islamiyya, Ummulkhairi, ta rasa ranta bayan wasu fusatattun matasa sun zarge ta da satar yara ba tare da gabatar da wata hujja da ta tabbatar da hakan ba.

Lamarin, wanda ya haifar da ɗimbin ce-ce-ku-ce da alhini a cikin al’umma, ya sake jawo hankali kan haɗarin yaɗa jita-jita da kuma ɗaukar doka a hannu, wani abu da masana da masu fafutukar kare haƙƙin Ɗan’adam ke ganin yana ƙara zama barazana ga zaman lafiya da adalci.

Duk da ƙoƙarin wasu mutane na ceto ta, lamarin ya rikiɗe zuwa tashin hankali wanda ya yi sanadiyyar rasa ranta. Al’ummar yankin da ƙungiyoyi daban-daban sun yi Allah-wadai da kisan tare da kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike domin gurfanar da masu hannu a wannan aika-aika.

ADVERTISEMENT

Marigayiyar ta bar gidanta a Sabon Garin Maraban Jos ne domin halartar wata muhadara da malamai suka shirya a makarantar Tashiyhul Iman da ke tsohuwar Maraba.

A cewar shaidun gani da ido, bayan abokan tafiyarta sun riga sun wuce gaba, sai ta tsaya tambayar hanyar zuwa wurin taron.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

 Ana zargin cewa yayin da take tambayar wasu yara hanyar, wasu mutane suka yi mata kallon shakku tare da fara yaɗa zargin cewa mai satar yara ce.

Cikin ƙanƙanin lokaci, jita-jitar ta bazu kamar wutar daji, lamarin da ya sa jama’a suka fara taruwa a kanta cikin fushi da zargi.

Da tashin hankalin ya fara ƙamari, jami’an tsaro sun kai Ummulkhairi ofishin ƴansanda domin kare lafiyarta tare da gudanar da bincike kan zargin da ake yi mata.

Shaidu sun shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa a lokacin da take hannun jami’an tsaro, wakilan iyalanta da wasu daga cikin danginta sun isa ofishin domin tabbatar da asalinta. Sun bayyana cewa fitacciyar malamar addini ce mai koyar da yara da mata ilimin addinin Musulunci, kuma babu wata hujja da ke nuna cewa ta aikata laifin da ake zarginta da shi.

Sai dai duk da wannan bayani da ƙoƙarin wasu masu ruwa da tsaki na kwantar da tarzoma, fushin wasu matasa bai lafa ba.

Shaidu sun bayyana cewa daga bisani lamarin ya rikice ya koma rikici, inda fusatattun matasa suka afka wa malamar.

Wani matasa mai suna Ukasha Umar wanda abin ya faru gabansa ya shaida wa wakilinmu cewa

 an yi mata dukan tsiya kafin daga bisani aka kashe ta tare da ƙona gawarta, abin da ya jefa iyalai, abokai, ɗalibai da ma al’ummar yankin cikin matsanancin jimami.

Ba ita kaɗai ba ce ta gamu da wannan iftila’i. Rahotanni sun kuma nuna cewa an ƙone babur ɗin wani malami da ya yi ƙoƙarin shiga tsakani domin cetonta daga hannun masu harin.

Bayan aukuwar lamarin, wasu bayanai da suka bazu a kafafen sada zumunta sun yi zargin cewa jami’an ƴansanda ne suka miƙa matar ga fusatattun matasa.

Sai dai mai magana da yawun rundunar ƴansandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya musanta wannan zargi.

A wata tattaunawa da manema labarai, ya ce jami’an tsaro sun yi bakin ƙoƙarinsu wajen kare rayuwar marigayiyar, kuma su ne suka fara cetonta daga hannun jama’a tun da farko.

Ya bayyana cewa wasu daga cikin manyan yankin ma sun yi iya ƙoƙarinsu wajen hana aukuwar lamarin, amma lamarin ya fi ƙarfin yadda ake zato.

Biyo bayan kisan gillar, gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa za ta ɗauki matakan da suka dace domin tabbatar da an yi adalci.

Shugaban ƙaramar hukumar Igabi, Sani Abdul, wanda ya ziyarci iyalan marigayiyar ya tabbatar da cewa gwamnati ta shiga cikin lamarin tare da bibiyar yadda abin ya faru wanda kuma za ta ɗauki matakan da suka kamata wajen daƙile yaɗuwar duk wata fitana.

Haka kuma, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Kaduna, Hajiya Rabi Salisu, ta jajanta wa iyalan marigayiyar tare da bayyana cewa gwamnati za ta tallafa musu a wannan lokaci na jimami.

Ta ce mutuwar Ummulkhairi ba kawai rasa rai ba ce, wani abin tunatarwa ne ga al’umma kan illar yanke hukunci bisa jita-jita da zarge-zarge marasa tushe.

Malama
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso
  • Sulaiman
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
  • Sulaiman
    Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027
Malama
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

MASU ALAKA

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027
Labarai

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Next Post
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Malama

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.