ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

by Sulaiman and Shehu Yahaya
2 hours ago
Malama

Wani mummunan al’amari da ya girgiza zukatan al’umma ya faru a yankin Maraban Jos da ke ƙaramar hukumar Igabi a Jihar Kaduna, inda wata malamar Islamiyya, Ummulkhairi, ta rasa ranta bayan wasu fusatattun matasa sun zarge ta da satar yara ba tare da gabatar da wata hujja da ta tabbatar da hakan ba.

Lamarin, wanda ya haifar da ɗimbin ce-ce-ku-ce da alhini a cikin al’umma, ya sake jawo hankali kan haɗarin yaɗa jita-jita da kuma ɗaukar doka a hannu, wani abu da masana da masu fafutukar kare haƙƙin Ɗan’adam ke ganin yana ƙara zama barazana ga zaman lafiya da adalci.

Duk da ƙoƙarin wasu mutane na ceto ta, lamarin ya rikiɗe zuwa tashin hankali wanda ya yi sanadiyyar rasa ranta. Al’ummar yankin da ƙungiyoyi daban-daban sun yi Allah-wadai da kisan tare da kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike domin gurfanar da masu hannu a wannan aika-aika.

ADVERTISEMENT

Marigayiyar ta bar gidanta a Sabon Garin Maraban Jos ne domin halartar wata muhadara da malamai suka shirya a makarantar Tashiyhul Iman da ke tsohuwar Maraba.

A cewar shaidun gani da ido, bayan abokan tafiyarta sun riga sun wuce gaba, sai ta tsaya tambayar hanyar zuwa wurin taron.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

 Ana zargin cewa yayin da take tambayar wasu yara hanyar, wasu mutane suka yi mata kallon shakku tare da fara yaɗa zargin cewa mai satar yara ce.

Cikin ƙanƙanin lokaci, jita-jitar ta bazu kamar wutar daji, lamarin da ya sa jama’a suka fara taruwa a kanta cikin fushi da zargi.

Da tashin hankalin ya fara ƙamari, jami’an tsaro sun kai Ummulkhairi ofishin ƴansanda domin kare lafiyarta tare da gudanar da bincike kan zargin da ake yi mata.

Shaidu sun shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa a lokacin da take hannun jami’an tsaro, wakilan iyalanta da wasu daga cikin danginta sun isa ofishin domin tabbatar da asalinta. Sun bayyana cewa fitacciyar malamar addini ce mai koyar da yara da mata ilimin addinin Musulunci, kuma babu wata hujja da ke nuna cewa ta aikata laifin da ake zarginta da shi.

Sai dai duk da wannan bayani da ƙoƙarin wasu masu ruwa da tsaki na kwantar da tarzoma, fushin wasu matasa bai lafa ba.

Shaidu sun bayyana cewa daga bisani lamarin ya rikice ya koma rikici, inda fusatattun matasa suka afka wa malamar.

Wani matasa mai suna Ukasha Umar wanda abin ya faru gabansa ya shaida wa wakilinmu cewa

 an yi mata dukan tsiya kafin daga bisani aka kashe ta tare da ƙona gawarta, abin da ya jefa iyalai, abokai, ɗalibai da ma al’ummar yankin cikin matsanancin jimami.

Ba ita kaɗai ba ce ta gamu da wannan iftila’i. Rahotanni sun kuma nuna cewa an ƙone babur ɗin wani malami da ya yi ƙoƙarin shiga tsakani domin cetonta daga hannun masu harin.

Bayan aukuwar lamarin, wasu bayanai da suka bazu a kafafen sada zumunta sun yi zargin cewa jami’an ƴansanda ne suka miƙa matar ga fusatattun matasa.

Sai dai mai magana da yawun rundunar ƴansandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya musanta wannan zargi.

A wata tattaunawa da manema labarai, ya ce jami’an tsaro sun yi bakin ƙoƙarinsu wajen kare rayuwar marigayiyar, kuma su ne suka fara cetonta daga hannun jama’a tun da farko.

Ya bayyana cewa wasu daga cikin manyan yankin ma sun yi iya ƙoƙarinsu wajen hana aukuwar lamarin, amma lamarin ya fi ƙarfin yadda ake zato.

Biyo bayan kisan gillar, gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa za ta ɗauki matakan da suka dace domin tabbatar da an yi adalci.

Shugaban ƙaramar hukumar Igabi, Sani Abdul, wanda ya ziyarci iyalan marigayiyar ya tabbatar da cewa gwamnati ta shiga cikin lamarin tare da bibiyar yadda abin ya faru wanda kuma za ta ɗauki matakan da suka kamata wajen daƙile yaɗuwar duk wata fitana.

Haka kuma, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Kaduna, Hajiya Rabi Salisu, ta jajanta wa iyalan marigayiyar tare da bayyana cewa gwamnati za ta tallafa musu a wannan lokaci na jimami.

Ta ce mutuwar Ummulkhairi ba kawai rasa rai ba ce, wani abin tunatarwa ne ga al’umma kan illar yanke hukunci bisa jita-jita da zarge-zarge marasa tushe.

Malama
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh
  • Sulaiman
    El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame
Malama
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

MASU ALAKA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Next Post
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.