Wani mummunan al’amari da ya girgiza zukatan al’umma ya faru a yankin Maraban Jos da ke ƙaramar hukumar Igabi a Jihar Kaduna, inda wata malamar Islamiyya, Ummulkhairi, ta rasa ranta bayan wasu fusatattun matasa sun zarge ta da satar yara ba tare da gabatar da wata hujja da ta tabbatar da hakan ba.
Lamarin, wanda ya haifar da ɗimbin ce-ce-ku-ce da alhini a cikin al’umma, ya sake jawo hankali kan haɗarin yaɗa jita-jita da kuma ɗaukar doka a hannu, wani abu da masana da masu fafutukar kare haƙƙin Ɗan’adam ke ganin yana ƙara zama barazana ga zaman lafiya da adalci.
Duk da ƙoƙarin wasu mutane na ceto ta, lamarin ya rikiɗe zuwa tashin hankali wanda ya yi sanadiyyar rasa ranta. Al’ummar yankin da ƙungiyoyi daban-daban sun yi Allah-wadai da kisan tare da kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike domin gurfanar da masu hannu a wannan aika-aika.
Marigayiyar ta bar gidanta a Sabon Garin Maraban Jos ne domin halartar wata muhadara da malamai suka shirya a makarantar Tashiyhul Iman da ke tsohuwar Maraba.
A cewar shaidun gani da ido, bayan abokan tafiyarta sun riga sun wuce gaba, sai ta tsaya tambayar hanyar zuwa wurin taron.
Ana zargin cewa yayin da take tambayar wasu yara hanyar, wasu mutane suka yi mata kallon shakku tare da fara yaɗa zargin cewa mai satar yara ce.
Cikin ƙanƙanin lokaci, jita-jitar ta bazu kamar wutar daji, lamarin da ya sa jama’a suka fara taruwa a kanta cikin fushi da zargi.
Da tashin hankalin ya fara ƙamari, jami’an tsaro sun kai Ummulkhairi ofishin ƴansanda domin kare lafiyarta tare da gudanar da bincike kan zargin da ake yi mata.
Shaidu sun shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa a lokacin da take hannun jami’an tsaro, wakilan iyalanta da wasu daga cikin danginta sun isa ofishin domin tabbatar da asalinta. Sun bayyana cewa fitacciyar malamar addini ce mai koyar da yara da mata ilimin addinin Musulunci, kuma babu wata hujja da ke nuna cewa ta aikata laifin da ake zarginta da shi.
Sai dai duk da wannan bayani da ƙoƙarin wasu masu ruwa da tsaki na kwantar da tarzoma, fushin wasu matasa bai lafa ba.
Shaidu sun bayyana cewa daga bisani lamarin ya rikice ya koma rikici, inda fusatattun matasa suka afka wa malamar.
Wani matasa mai suna Ukasha Umar wanda abin ya faru gabansa ya shaida wa wakilinmu cewa
an yi mata dukan tsiya kafin daga bisani aka kashe ta tare da ƙona gawarta, abin da ya jefa iyalai, abokai, ɗalibai da ma al’ummar yankin cikin matsanancin jimami.
Ba ita kaɗai ba ce ta gamu da wannan iftila’i. Rahotanni sun kuma nuna cewa an ƙone babur ɗin wani malami da ya yi ƙoƙarin shiga tsakani domin cetonta daga hannun masu harin.
Bayan aukuwar lamarin, wasu bayanai da suka bazu a kafafen sada zumunta sun yi zargin cewa jami’an ƴansanda ne suka miƙa matar ga fusatattun matasa.
Sai dai mai magana da yawun rundunar ƴansandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya musanta wannan zargi.
A wata tattaunawa da manema labarai, ya ce jami’an tsaro sun yi bakin ƙoƙarinsu wajen kare rayuwar marigayiyar, kuma su ne suka fara cetonta daga hannun jama’a tun da farko.
Ya bayyana cewa wasu daga cikin manyan yankin ma sun yi iya ƙoƙarinsu wajen hana aukuwar lamarin, amma lamarin ya fi ƙarfin yadda ake zato.
Biyo bayan kisan gillar, gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa za ta ɗauki matakan da suka dace domin tabbatar da an yi adalci.
Shugaban ƙaramar hukumar Igabi, Sani Abdul, wanda ya ziyarci iyalan marigayiyar ya tabbatar da cewa gwamnati ta shiga cikin lamarin tare da bibiyar yadda abin ya faru wanda kuma za ta ɗauki matakan da suka kamata wajen daƙile yaɗuwar duk wata fitana.
Haka kuma, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Kaduna, Hajiya Rabi Salisu, ta jajanta wa iyalan marigayiyar tare da bayyana cewa gwamnati za ta tallafa musu a wannan lokaci na jimami.
Ta ce mutuwar Ummulkhairi ba kawai rasa rai ba ce, wani abin tunatarwa ne ga al’umma kan illar yanke hukunci bisa jita-jita da zarge-zarge marasa tushe.














