An bude taro na 13 na ministocin kula da yawon bude ido na kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki ta kasashen Asiya da tekun Pasifik wato APEC a takaice a jiya Asabar, a yankin musammam na Macao na kasar Sin.
Yayin taron, wakilai sun lalubo hanyoyin amfani da kirkire-kirkiren dijital da zurfafa hadin gwiwa domin bunkasa bangaren yawon bude ido na yankin. Yayin taron mai taken Kirkire-Kirkiren Dijital, Karfin Hadin Gwiwa: Cin Gajiyar Bangaren Yawon Bude Ido Domin Al’ummar Asiya da tekun Pasifik, shugabannin hukumomin yawon bude ido daga kasashe 21 na APEC, sun yi musayar ra’ayi kan rawar da fasahohin zamani ke takawa wajen bunkasa yawon bude ido da ma tattalin arziki da zamantakewa.
A cewar wakilan, bangaren yawon bude ido na zaman wani muhimmin karfin bunkasa tattalin arzikin yankin, suna cewa, yana tattare da abubuwa masu karfi da damarmakin da ba a kai ga amfana da su ba da makoma mai haske.
Da suke bayyana taron ministocin a matsayin wani muhimmin bangare na shekarar da kasar Sin ke jagorantar kungiyar APEC, wakilan sun ce taron wani sabon mafari ne na zurfafa hadin gwiwa a bangaren yawon bude ido tsakanin kasashe mambobi.
A matsayin wani bangare na taron ministocin, an gudanar da taro na 67 na rukunin nazarin ayyukan yawon bude ido na kungiyar a ranekun Laraba da Alhamis, a yankin musamman na Macao.
Bugu da kari, a matsayin mai shugabantar APEC a bana, kasar Sin za ta karbi bakuncin taron shugabannin kasashen kungiyar na 33 a birnin Shenzhen na lardin Guandong a watan Nuwamba. Kimanin taruka da shirye-shirye 300 masu alaka da APEC za a gudanar a biranen kasar Sin a bana. (Fa’iza Mustapha)













