Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayiya Ummulkhairi Usman Aliyu, wadda wasu fusatattun mutane suka kashe bisa zargin satar yara a yankin Maraban Jos da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a shafinsa na Facebook bayan ziyarar da ya kai wa iyalan marigayiyar a ranar Asabar da yamma domin jajanta musu da kuma nuna goyon bayan gwamnati a wannan lokaci na tsananin baƙin ciki.
A cewarsa, gwamnatin jihar za ta tabbatar an gudanar da cikakken bincike tare da gurfanar da duk wanda ke da hannu a kisan a gaban kotu domin a hukunta su bisa doka.
Haka kuma, Gwamna Sani ya yi alƙawarin cewa gwamnatin jihar za ta ɗauki nauyin ilimi da walwalar ‘ya’yan marigayiyar domin rage wa iyalanta radadin rashin da suka yi.
Rahotanni sun nuna cewa marigayiyar, wacce malamar addinin Musulunci ce, ta ɓata hanya ne yayin da take kan hanyarta ta zuwa wani taro a ranar 21 ga Yuni, 2026, kafin wasu mutane su zarge ta da satar yara. Duk da cewa tana hannun jami’an tsaro a Maraban Jos, amma an ƙwace ta daga wurinsu sannan aka yi mata dukan tsiya har ta rasa ranta.
Lamarin ya haifar da damuwa da kira daga al’umma da kungiyoyin kare haƙƙin bil’adama kan buƙatar dakile hukuncin daukar doka a hannu da tabbatar da cewa ana barin hukumomin tsaro da kotuna su gudanar da aikinsu bisa doka.













