Rundunar Ƴansandan Jihar Kogi ta ƙaddamar da bincike mai zurfi kan kisan gillar da aka yi wa wata malama, Maryam Usman, wadda aka yi wa duka har lahira a garin Lokoja. Wannan mummunan lamari ya auku ne bayan da malamar, wadda ke koyarwa a makarantar “Muslim Community Nursery and Primary School”, ta ladabtar da wani ɗalibi saboda saɓa dokar makaranta, lamarin da ya sa ɗalibin ya tafi gida ya kira danginsa domin su ɗauki fansa.
Daily Trust ta bayyana cewa mahaifiyar ɗalibin tare da yayyensa maza sun biyo malamar har gidanta da ke unguwar Sarkin Noma a Lokoja, inda suka far mata da duka da itace ba kaukauta. Suka yi mata dukan tsiya a gaban mutane har sai da ta suma, inda daga baya aka garzaya da ita asibiti amma aka tabbatar da cewa ta rasu sakamakon raunin da ta samu a kanta.
Wannan ɗanyen aiki ya tayar da hankulan mazauna garin Lokoja da ɗaukacin ƙungiyoyin malamai na jihar, waɗanda suka fito fili suka yi Allah-wadai da kisan tare da neman gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa na kare rayukan malamai. Iyalin marigayiyar Maryam Usman da shugabannin al’umma sun yi kiran da a gaggauta kamo waɗanda suka aikata wannan kisa domin yi wa malamar adalci.
Kakakin rundunar ƴansandan jihar ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa jami’an tsaro suna can suna farautar mutanen da suka aikata kisan waɗanda tuni suka tsere bayan sun gama tafka wannan ta’asa.
Rundunar ta yi gargaɗin cewa ba za ta lamunci irin wannan ɗaukar doka a hannu ba, kuma za a gurfanar da duk wanda aka kama a gaban kotu domin fuskantar hukuncin kisan kai.














