Jami’an Hukumar tsaro ta DSS a Kano sun kama ɗaya daga cikin waɗanda suka shirya sace mahaifiyar fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara. Yayin artabun guda daga cikin masu garkuwar ya mutu wani wanda ake zargi da kuma samun kudi har ₦26.5 miliyan.
Wani babban jami’i a hukumar DSS ya bayyana cewa, tawagar musamman ta DSS, bisa ga bayanan sirri masu inganci, sun kama wata tawaga ta ‘yan bindiga biyar a dajin Maƙarfi yayin da suke raba kuɗin fansa. An kama ɗaya daga cikin su, Hamisu Tukur, da raunin harbin bindiga, yayin da aka kashe wani wanda ake zargi, Bature.
- Aisha Humaira Ta Mayar Da Martani Kan Sace Mahaifiyar Rarara
- Mahaifiyar Rarara Ta Kubuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga
Lamarin sacewar ya faru ne makonni uku da suka gabata lokacin da wasu ‘yan bindiga suka shiga gidan Hajiya Hauwa’u Adamu, mahaifiyar Rarara, a Kahutu, suka yi garkuwa da ita.
Ta samu ‘yancinta bayan ta shafe kwanaki 20 a hannun masu garkuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp