Kotun Ƙoli ta Nijeriya za ta yanke hukunci yau kan ƙarar ɗaukaka ƙara da ɓangaren PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki da kuma ta ADC suka shigar dangane da rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyun biyu.
Kotun kolin, wadda ta yi zama kan batun ƙararrakin a ranar 22 ga Afrilu, inda tace, za ta sanar da ranar yanke hukunci daga baya, ta sanya yau (Alhamis) a matsayin ranar yanke hukunci kan ƙarar guda biyu.
Ɗaukaka ƙarar Turaki mai lamba SC/CV/164/2026 na neman soke hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, waɗanda suka soke taron babban taron ƙasa na jam’iyyar da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025, wanda ya samar da shugabannin ɓangaren Turaki.
Yayin gabatar da hujjojinsu da aka shigar ranar 2 ga Afrilu, lauyoyin masu ɗaukaka ƙarar ƙarƙashin jagorancin Paul Erokoro, SAN, sun roƙi Kotun Ƙoli ba kawai ta amince da ƙarar tasu ba, har ma ta yi watsi da wata ƙarar martani da wani ɓangaren jam’iyyar mai alaƙa da Ministan Babban Birnin Tarayya ya shigar.
Kotun kolin ta kuma sanar da cewa za ta yanke hukunci yau kan ƙarar da shugaban ADC na ƙasa, David Mark, ya shigar kan Nafiu Bala Gombe, tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar na ƙasa.
A cikin ƙarar mai lamba SC/CV/180/2026, David Mark na ƙalubalantar ikon kotu wajen tsoma baki cikin harkokin cikin gida na jam’iyyar.
Tsohon shugaban Majalisar Dattawan na kuma neman Kotun Ƙoli ta dakatar da hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara da aka yanke ranar 12 ga Maris, wanda ya yi watsi da ƙarar da ya shigar dangane da rikicin shugabanci da ke gudana a jam’iyyar.















Discussion about this post