ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano

by Muhammad Bashir and Sulaiman
2 months ago
Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da kashe Naira biliyan 21.29 domin gyara da farfaɗo da manyan cibiyoyin samar da ruwa a faɗin jihar, a wani mataki na magance matsalar ƙarancin ruwa da ta daɗe tana addabar al’umma.

Ma’aikatar Albarkatun Ruwa ta jihar ce ta sanar da hakan a wata sanarwa da Mukaddashin Kwamishina, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ya fitar a ranar 30 ga Afrilu, 2026.A cewar sanarwar, aikin zai mayar da hankali ne kan manyan cibiyoyin Tamburawa, Challawa da kuma Goron Dutse, waɗanda tabarbarewar aikinsu ta janyo ƙarancin ruwa a sassa da dama na jihar.

Sanarwar ta ce daga cikin ayyukan da za a gudanar akwai gyaran matatar ruwan Tamburawa da kuma dawo da famfon tace ruwa kan kuɗin Naira biliyan 9.9. Haka kuma za a gyara famfon tace ruwa na Challawa da matatar ruwan, tare da farfaɗo da tankunan ruwan Goron Dutse kan kuɗin Naira biliyan 11.39.

ADVERTISEMENT

Dakta Hashim ya bayyana wannan mataki a matsayin ɗaya daga cikin manyan jarin da aka taɓa zuba a ɓangaren ruwa a ‘yan shekarun nan, yana mai cewa matakin ya zama dole cikin gaggawa.

Ya ce matatar ruwan Tamburawa, wadda aka gina domin samar da lita miliyan 150 na ruwa a rana, a halin yanzu tana aiki ne da kusan kashi 27 cikin ɗari kacal, sakamakon lalacewar da ambaliya ta haddasa tun daga shekarar 2022.Haka zalika, matatar Challawa wadda ke da ƙarfin samar da lita miliyan 220 a rana, tana aiki ne da ƙasa da kashi 30 cikin ɗari.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

A cewarsa, a haɗe, matatun biyu an gina su domin samar da lita miliyan 370 na ruwa a kullum, amma a yanzu suna samar da ƙasa da hakan, lamarin da ke haifar da ƙarancin ruwa a sassa da dama na jihar.

Bugu da ƙari, tankunan ruwan Goron Dutse, waɗanda ke taka muhimmiyar rawa wajen rarraba ruwa a yawancin yankunan birnin Kano, sun daina aiki gaba ɗaya sakamakon lalata muhimman kayan aikinsu.

“Waɗannan matsaloli ne da ke bayyana girman ƙalubalen da muke fuskanta. Amma kuma su ne ginshiƙin shirin da muka ɗauka domin magance matsalar gaba ɗaya,” in ji Dakta Hashim.

Ya tabbatar wa al’umma cewa ayyukan da aka amince da su za su ƙara yawan samar da ruwa, su inganta rarrabawa, tare da daidaita wadatar ruwa a faɗin Kano.Duk da sanin hali da wahalhalun da jama’a ke fuskanta, kwamishinan ya jaddada cewa gwamnan jihar na da ƙudurin warware matsalar ta zama tarihi.

“Gwamna Abba Kabir Yusuf na da niyyar magance wannan matsala ta hanyar da za ta ɗore, kuma muna da yakinin cewa da waɗannan matakai, za a rage matsalar ƙarancin ruwa a Kano har ta kau gaba ɗaya,” in ji shi.

Haka kuma ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen kare kayan aikin ruwa daga lalata su, yana mai cewa hakan na daga cikin abubuwan da ke haddasa yawaitar matsalolin samar da ruwa.

Gwamnatin Jihar Kano ta kuma sake jaddada aniyarta na samar da ingantaccen ruwan sha ga al’umma tare da inganta rayuwarsu ta hanyar ci gaba da zuba jari a muhimman ayyukan more rayuwa.

Yusuf
Muhammad Bashir
+ posts Bio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga
Yusuf
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo
  • Sulaiman
    Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Next Post
Kar Ku Tayar Da Hankulanku, Mun Samo Fetur Fiye Da Lita Biliyan 1.5 – NNPCL

Ɓatan Dabon Naira Tiriliyan 210 A NNPCL: Kyari, Ajia da Wunti Sun Shirya Bayar Da Shaida

LABARAI MASU NASABA

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.