Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da kashe Naira biliyan 21.29 domin gyara da farfaɗo da manyan cibiyoyin samar da ruwa a faɗin jihar, a wani mataki na magance matsalar ƙarancin ruwa da ta daɗe tana addabar al’umma.
Ma’aikatar Albarkatun Ruwa ta jihar ce ta sanar da hakan a wata sanarwa da Mukaddashin Kwamishina, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ya fitar a ranar 30 ga Afrilu, 2026.A cewar sanarwar, aikin zai mayar da hankali ne kan manyan cibiyoyin Tamburawa, Challawa da kuma Goron Dutse, waɗanda tabarbarewar aikinsu ta janyo ƙarancin ruwa a sassa da dama na jihar.
Sanarwar ta ce daga cikin ayyukan da za a gudanar akwai gyaran matatar ruwan Tamburawa da kuma dawo da famfon tace ruwa kan kuɗin Naira biliyan 9.9. Haka kuma za a gyara famfon tace ruwa na Challawa da matatar ruwan, tare da farfaɗo da tankunan ruwan Goron Dutse kan kuɗin Naira biliyan 11.39.
Dakta Hashim ya bayyana wannan mataki a matsayin ɗaya daga cikin manyan jarin da aka taɓa zuba a ɓangaren ruwa a ‘yan shekarun nan, yana mai cewa matakin ya zama dole cikin gaggawa.
Ya ce matatar ruwan Tamburawa, wadda aka gina domin samar da lita miliyan 150 na ruwa a rana, a halin yanzu tana aiki ne da kusan kashi 27 cikin ɗari kacal, sakamakon lalacewar da ambaliya ta haddasa tun daga shekarar 2022.Haka zalika, matatar Challawa wadda ke da ƙarfin samar da lita miliyan 220 a rana, tana aiki ne da ƙasa da kashi 30 cikin ɗari.
A cewarsa, a haɗe, matatun biyu an gina su domin samar da lita miliyan 370 na ruwa a kullum, amma a yanzu suna samar da ƙasa da hakan, lamarin da ke haifar da ƙarancin ruwa a sassa da dama na jihar.
Bugu da ƙari, tankunan ruwan Goron Dutse, waɗanda ke taka muhimmiyar rawa wajen rarraba ruwa a yawancin yankunan birnin Kano, sun daina aiki gaba ɗaya sakamakon lalata muhimman kayan aikinsu.
“Waɗannan matsaloli ne da ke bayyana girman ƙalubalen da muke fuskanta. Amma kuma su ne ginshiƙin shirin da muka ɗauka domin magance matsalar gaba ɗaya,” in ji Dakta Hashim.
Ya tabbatar wa al’umma cewa ayyukan da aka amince da su za su ƙara yawan samar da ruwa, su inganta rarrabawa, tare da daidaita wadatar ruwa a faɗin Kano.Duk da sanin hali da wahalhalun da jama’a ke fuskanta, kwamishinan ya jaddada cewa gwamnan jihar na da ƙudurin warware matsalar ta zama tarihi.
“Gwamna Abba Kabir Yusuf na da niyyar magance wannan matsala ta hanyar da za ta ɗore, kuma muna da yakinin cewa da waɗannan matakai, za a rage matsalar ƙarancin ruwa a Kano har ta kau gaba ɗaya,” in ji shi.
Haka kuma ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen kare kayan aikin ruwa daga lalata su, yana mai cewa hakan na daga cikin abubuwan da ke haddasa yawaitar matsalolin samar da ruwa.
Gwamnatin Jihar Kano ta kuma sake jaddada aniyarta na samar da ingantaccen ruwan sha ga al’umma tare da inganta rayuwarsu ta hanyar ci gaba da zuba jari a muhimman ayyukan more rayuwa.














Discussion about this post