ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ‘yan jarida da su guji tallata ’yan ta’adda da ‘yan bindiga da sauran miyagu da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasar nan.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin zama na bakwai na Jerin Zauren Bayanai na Ministoci na shekarar 2025 wanda aka gudanar a Cibiyar Yaɗa Labarai ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Jirgin Farko Daga Minna Zuwa Abuja Ya Nuna Haɗin Gwiwar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi – Minista
  • Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Idris ya ce, “Kafofin yaɗa labarai, a matsayin su na masu tantance labarai kuma abokan hulɗa wajen gina ƙasa, suna da muhimmiyar rawar da za su taka wajen ƙarfafa gwiwar dakarun mu ta hanyar nuna irin nasarorin da suka samu da sadaukarwar da suke yi.

ADVERTISEMENT

“Dole ne mu guji tallata waɗannan ƙungiyoyi. Dole ne mu cire su daga shafukan farko na jaridu, mu riƙa bayar da rahoto a kan su daidai da yadda suke — wato masu laifi ne — ba tare da ƙawata ayyukan su ko ba da muhimmanci ga ƙarya da farfagandar da suke yaɗawa ba.”

Ministan ya ƙara da cewa ‘yan ta’adda da sauran miyagun ƙungiyoyi suna amfani da kafafen watsa labarai da na sada zumunta ne domin su yaɗa fargaba da ƙarya da kuma jawo mutane zuwa gare su.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Saboda haka, ya buƙaci ’yan jarida da editoci da su zama masu kishin ƙasa da ƙwarewa wajen bayar da rahoto, ta hanyar guje wa manyan kanun labarai masu tayar da hankali da kuma ƙin zama hanyar yaɗa farfaganda ta masu aikata ta’addanci.

Ya ce: “Waɗannan ba ‘yan gwagwarmayar ‘yanci ba ne; masu kisa ne, masu sace mutane ne, masu ɓarna ne, kuma dole ne a bayyana su a hakan.”

Ministan ya kuma haskaka wani muhimmin ɓangare na Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, musamman ɓangaren da ya shafi “Ƙarfafa Tsaron Ƙasa Don Samar Da Zaman Lafiya Da Cigaba.”

Ya ce Gwamnatin Tarayya tana ci gaba da kashe kuɗi wajen samar da kayan aiki na zamani ga sojoji, da inganta binciken leƙen asiri da kuma haɓaka haɗin gwiwa da ƙasashen duniya.

Idris ya bayyana cewa Jerin Zauren Bayanai na Ministocin wani shiri ne da ma’aikatar sa ta ƙirƙira domin bai wa ministoci dama su faɗa wa ’yan Nijeriya irin nasarorin da suke samu, da ayyukan da ke gudana da kuma tsare-tsaren da za su aiwatar a nan gaba.

Ya ce, “Ta wannan dandali na tattaunawa, wanda ake watsawa kai-tsaye a tashoshin talbijin na ƙasa da kuma kafafen sada zumunta, muna ci gaba da nuna jajircewar mu ga gaskiya, ɗaukar nauyi, da haɗin kai da jama’a.”

Ministan ya yaba wa kafafen yaɗa labarai bisa goyon bayan da suke ba wannan shiri da kuma rawar da suke takawa wajen wayar da kan al’umma game da ayyukan gwamnati.

A taron, Ministan Tsaro, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, da Ministan Muhalli, Alhaji Balarabe Abbas, sun gabatar da bayanai ga manema labarai kan nasarorin da ma’aikatun su suke samu.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Duniya Ta Gano Damammaki Masu Kyau Daga Kasuwar Kasar Sin A Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Ta Duniya

Duniya Ta Gano Damammaki Masu Kyau Daga Kasuwar Kasar Sin A Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.