ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ‘yan jarida da su guji tallata ’yan ta’adda da ‘yan bindiga da sauran miyagu da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasar nan.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin zama na bakwai na Jerin Zauren Bayanai na Ministoci na shekarar 2025 wanda aka gudanar a Cibiyar Yaɗa Labarai ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Jirgin Farko Daga Minna Zuwa Abuja Ya Nuna Haɗin Gwiwar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi – Minista
  • Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Idris ya ce, “Kafofin yaɗa labarai, a matsayin su na masu tantance labarai kuma abokan hulɗa wajen gina ƙasa, suna da muhimmiyar rawar da za su taka wajen ƙarfafa gwiwar dakarun mu ta hanyar nuna irin nasarorin da suka samu da sadaukarwar da suke yi.

ADVERTISEMENT

“Dole ne mu guji tallata waɗannan ƙungiyoyi. Dole ne mu cire su daga shafukan farko na jaridu, mu riƙa bayar da rahoto a kan su daidai da yadda suke — wato masu laifi ne — ba tare da ƙawata ayyukan su ko ba da muhimmanci ga ƙarya da farfagandar da suke yaɗawa ba.”

Ministan ya ƙara da cewa ‘yan ta’adda da sauran miyagun ƙungiyoyi suna amfani da kafafen watsa labarai da na sada zumunta ne domin su yaɗa fargaba da ƙarya da kuma jawo mutane zuwa gare su.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Saboda haka, ya buƙaci ’yan jarida da editoci da su zama masu kishin ƙasa da ƙwarewa wajen bayar da rahoto, ta hanyar guje wa manyan kanun labarai masu tayar da hankali da kuma ƙin zama hanyar yaɗa farfaganda ta masu aikata ta’addanci.

Ya ce: “Waɗannan ba ‘yan gwagwarmayar ‘yanci ba ne; masu kisa ne, masu sace mutane ne, masu ɓarna ne, kuma dole ne a bayyana su a hakan.”

Ministan ya kuma haskaka wani muhimmin ɓangare na Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, musamman ɓangaren da ya shafi “Ƙarfafa Tsaron Ƙasa Don Samar Da Zaman Lafiya Da Cigaba.”

Ya ce Gwamnatin Tarayya tana ci gaba da kashe kuɗi wajen samar da kayan aiki na zamani ga sojoji, da inganta binciken leƙen asiri da kuma haɓaka haɗin gwiwa da ƙasashen duniya.

Idris ya bayyana cewa Jerin Zauren Bayanai na Ministocin wani shiri ne da ma’aikatar sa ta ƙirƙira domin bai wa ministoci dama su faɗa wa ’yan Nijeriya irin nasarorin da suke samu, da ayyukan da ke gudana da kuma tsare-tsaren da za su aiwatar a nan gaba.

Ya ce, “Ta wannan dandali na tattaunawa, wanda ake watsawa kai-tsaye a tashoshin talbijin na ƙasa da kuma kafafen sada zumunta, muna ci gaba da nuna jajircewar mu ga gaskiya, ɗaukar nauyi, da haɗin kai da jama’a.”

Ministan ya yaba wa kafafen yaɗa labarai bisa goyon bayan da suke ba wannan shiri da kuma rawar da suke takawa wajen wayar da kan al’umma game da ayyukan gwamnati.

A taron, Ministan Tsaro, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, da Ministan Muhalli, Alhaji Balarabe Abbas, sun gabatar da bayanai ga manema labarai kan nasarorin da ma’aikatun su suke samu.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Duniya Ta Gano Damammaki Masu Kyau Daga Kasuwar Kasar Sin A Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Ta Duniya

Duniya Ta Gano Damammaki Masu Kyau Daga Kasuwar Kasar Sin A Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.