Majalisar Dattawan Nijeriya ta buƙaci Babban Hafsan Sojin Ƙasa da Sufeto Janar na ’Yansanda da su gaggauta tura ƙarin jami’an tsaro zuwa al’ummomin da ke Jihar Benuwe domin dakile hare-haren ’yan bindiga da ke ci gaba da cin rayukan mutane.
Kiran ya shafi al’ummomin Akpachi-Ugboju, Otukpo-Nobi da Ondo Ugboju, inda hare-haren suka yi kamari.
Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a hare-haren da aka kai tsakanin ranar Juma’ar makon da ya gabata zuwa ranar Talata, kamar yadda ke ƙunshe cikin wani ƙuduri na gaggawa da Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar Dattawa, Abba Moro, ya gabatar a ranar Laraba.
Majalisar ta yi Allah wadai da hare-haren da aka kai kan al’ummomin da ba suji basu gani ba, tare da yin kira ga shugabannin hukumomin tsaro, musamman rundunar soji da ta ’yansanda, da su tura jami’ansu cikin gaggawa domin dawo da zaman lafiya da kuma kamo tare da gurfanar da masu hannu a hare-haren.














