A yau Laraba ne kwararru biyu a fannin kandagarkin cututtuka na kasar Sin da hukumar kula da cututtuka ta Sin ta zaba, suka tashi daga birnin Beijing zuwa kasar Uganda, bisa gayyatar “Tawagar tallafawa aikin yaki da cutar Ebola” ko IMST, wadda cibiyar kula da cututtuka ta Afirka, da hukumar lafiya ta duniya WHO suka kafa.
Ana sa ran kwararrun za su shiga hadakar kasa da kasa mai yaki da cutar Ebola a kasar.A ranar 17 ga watan Mayu ne hukumar WHO, ta ayyana cutar Ebola da ta barke a jamhuriyar dimokuradiyyar Kongo da Uganda a matsayin “matsalar lafiya ta gaggawa ta duniya”. Don daidaita ayyukan kandagarkin cutar, cibiyar kula da cututtuka ta Afirka, da WHO, sun hada kai wajen kafa tawagar IMST, wadda ta kunshi kungiyoyin aiki 14, ciki har da rukunonin daidaitawa da na gudanarwa, da kuma rukunonin aiki a dakin gwaje-gwaje, da gwajin kwayoyin cuta da sauransu, don samar da karfin hadin gwiwa na kasashe da yawa wajen yaki da cutar.
Kwararrun Sinawan biyu, za su shiga tsarin IMST ta hanyar bayar da tallafin fasaha, inda za su hada kai da kwararrun cibiyar kula da cututtuka ta Afirka, da WHO, da sauran kasashe wajen gudanar da nazarin bayanai, kimanta hadari da kuma tsara shawarwarin fasaha.
Wani jami’in hukumar kula da cututtuka ta kasar Sin wanda batun ya shafa, ya bayyana cewa zabar kwararrun da aka tura Uganda, don shiga hadakar IMST, wani aiki ne na a zo a gani wanda Sin ta shiga domin goyon bayanta ga yaki da cutar a Afirka. (Amina Xu)














