Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Lin Jian, ya ce a halin yanzu an hada tsarin samar da kayayyaki da na ayyukan masana’antu sosai a duniya, lamarin da ke samar da al’umma mai muradu na bai daya inda ake samun wadata ko shan wahala tare.
Ya ce ra’ayin neman raba-gari da sauran kasashe, zai kawo mummuan tasiri ga bangarorin da ke da wannan ra’ayi, tare da rage muradunsu.
Bugu da kari, game da sanarwar da wasu jami’an Amurka suka yi kwanan nan da ke bayyana goyon bayan dokar da za ta hukunta masu sayen man fetur daga Rasha, Lin Jian ya bayyana cewa Sin tana adawa da takunkumi ba bisa ka’ida ba na bangare daya, wanda ba shi da tushe a cikin dokokin kasa da kasa kuma bai samu amincewar MDD ba, yana cewa Sin za ta dauki duk matakan da suka wajaba don kare hakkokin kamfanoni da ’yan kasarta bisa ka’ida.
Ban da haka kuma, a gun taron, Lin Jian ya kuma gabatar da wasu bayanai game da bikin Makon Dijital na kungiyar APEC da za a gudanar a birnin Chengdu na lardin Sichuan a gobe Alhamis.(Safiyah Ma)














