Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya raba filaye 1,540 tare da tallafin kuɗi na Naira miliyan 100 ga shugabannin Ƙungiyar masu kula da Rumfunan Zaɓe na Jam’iyyar APC, wadda aka fi sani da ’Yan Akwati, a wani mataki na ƙarfafa tsarin jam’iyyar a matakin rumfunan zaɓe gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba.
Gwamna Yusuf ya bayyana tallafin ne yayin ƙaddamar da ƙungiyar ta ’Yan Akwati a hukumance, inda ya bayyana cewa tsarin rumfunan zaɓe shi ne ginshiƙin nasarar jam’iyyar APC a zaɓe.
Ya ce ƙarfafa magoya bayan jam’iyyar a matakin ƙasa zai taimaka wajen inganta wayar da kan jama’a da tattara ƙuri’u, tare da tabbatar da nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wa’adin mulkinsa na biyu, da kuma sauran ’yan takarar APC a zaɓuɓɓuka masu zuwa.
Gwamnan ya ƙara da cewa sake zaɓen Shugaba Tinubu zai tabbatar da ci gaba da aiwatar da sauye-sauye a fannin tattalin arziki da shirye-shiryen bunƙasa ƙasa da gwamnatin tarayya ta fara.
A cewarsa, rabon filayen da kuma tallafin Naira miliyan 100 an yi su ne domin ƙara wa mambobin ƙungiyar ƙwarin gwiwa, tare da ba su damar gudanar da ayyukan jam’iyya yadda ya kamata a matakin rumfunan zaɓe.
Tun da farko, Mai Bai Wa Gwamna Shawara kan Harkokin Siyasa, Mustapha Hamza Buhari Bakwana, ya bayyana cewa wannan tallafi shi ne kashi na farko kuma wani babban shiri da gwamnatin ke aiwatarwa domin ƙarfafa guiwar jam’iyyar APC a faɗin jihar kafin zaɓen 2027.
Ya bayyana kwarin guiwar cewa ƙungiyar ’Yan Akwati na da shirin tattara sama da ƙuri’u miliyan ɗaya ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Jihar Kano.
Taron ya samu halartar shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa, da wakilan ƙungiyar daga dukkan ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano.













