Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan ware Naira biliyan 6.44 a cikin kasafin kuɗin gwamnati domin abin da aka bayyana a matsayin “Tallafin Ƙungiyar Shugaban Ƙasa Ga Wasannin Neman Tikitin Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026”, yana tambayar dalilin wannan kasafi bayan da tawagar Super Eagles ta gaza samun gurbin shiga gasar.
A cikin wata sanarwa da kakakinsa, Phrank Shaibu, ya fitar a ranar Laraba, Atiku ya ce ware irin wannan maƙudan kuɗi, waɗanda aka ce an tanade su domin sufuri, sansanin horo da alawus-alawus na wasa, ya nuna gazawa wajen tsara kasafin kuɗi, ganin cewa Nijeriya ba ta kai ga buga gasar ba.
Ya yi tambaya da cewa, “Ta yaya gwamnati mai muhimmanci za ta ware Naira biliyan 6.44 domin tallafin neman tikitin Gasar Cin Kofin Duniya bayan ƙasar ta riga ta fice daga gasar? Wace gasa aka shirya a tallafa wa? Wa ya saka wannan tanadi cikin kasafin kuɗi, wa ya amince da shi, kuma wa ake sa ran zai amfana da kuɗin da manufarsa ta riga ta zama ba ta da amfani?”
Atiku ya bayyana cewa wannan ba kawai kuskuren yanke hukunci ba ne, amma alama ce da ke nuna matsala a tsarin shirya kasafin kuɗin ƙasa. Ya ce hakan na ƙara tabbatar da zargin jama’a cewa kasafin kuɗin gwamnati ya zama wurin saka kashe-kuɗaɗe marasa tushe da almubazzaranci da kuɗaɗen jama’a.
Ya ƙara da cewa, duba da irin matsin tattalin arzikin da ƙasar ke fuskanta, bai kamata gwamnati ta riƙa ɗaukar kuɗaɗen jama’a da wasa ba.
Atiku ya kuma yi kira ga majalisar tarayya da ta binciki yadda aka tsara da kuma yadda ake shirin kashe wannan kuɗi, tare da tabbatar da cewa an karkatar da su zuwa muhimman buƙatun ƙasa maimakon a kashe su kan gasar da Nijeriya ba ta cikin masu halarta.














