• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Kudiri 120 Cikin Wata Shida – Hon. Tajudeen

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisar wakilai

Shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, ya yaba wa ayyukan majalisar ta 10, inda ya ce a cikin watanni 6 shida na farko tun bayan kaddamar da majalisar a ranar 13 ga watan Yunin 2003, sun amince da kudurori 120.

Ya bayyana hakan ne da yake jawabi a wurin zaman hutu na majalisar wakilai da ya gudana ranar Asabar.

  • Yadda ANA Ta Shugabanci Gangamin Saukaka Zuwa Hajjin 2024 A Nijeriya
  • Kasashen Afirka Na Fadada Cudanya Da Kasar Sin A Fannoni Daban Daban

Haka kuma Abbas ya yaba wa abokan aikinsa bisa yadda suka nuna kwarewa da kuzari a cikin watanni shida da suka gabata.
“Sakamakon da muka samu a zauren majalisar wakilai a cikin watanni shida da suka gabata na da ban mamaki. Majalisar ta samu gabatar da kudurori 962 da muhawara 500 da kuma korafe-korafe 153.

“A cikin wadannan kudurori 120 sun tsallake karatu na biyu. A halin yanzu ana ci gaba da bita da kuma gyare-gyare don magance wasu matsalolin da aka taso da su yayin muhawarar,” inji shi.

Ya kuma kara da cewa an mika wasu kudirori 120 ga kwamitoci domin yin nazari mai zurfi a kai.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

A cewarsa, “Mun samu nasarar zartar da wasu kudirori da dama wadanda aka mika wa majalisar dattawa domin su yi aiki a kai.
“A cikin wadannan kudurorin akwai dokar lantarki da ka yi wa kwaskwarima ta 2023 da dokar binciken ma’aikatar tarayya da aka yi wa gyara ta 2023 da dokar kayyade kudade ta 2023 da aka yi wa gyaran fuska da dokar rantsuwa ta 2023.

“Sauran wasu muhimman kudirori da majalisar ta zartar sun hada da dokar hana haduwar kananan makamai da ta 2023, dokar hukumar kashe gobara ta tarayya ta 2023, dokar gudanar da shari’a kan manyan laifuka ta 2023, dokar hukumar raya yankin Neja Delta, kudirin dokar kafa majalisar binciken likitocin Nijeriya ta 2023, dokar kafa hukumar samar da zaman lafiya ta Nijeriya ta 2023 da kuma dokar kafa hukumar raya yankin kudu maso gabas ta 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Tinubu

Kasafin 2024: Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Rika Ba Da Rahoton Ayyukansu Duk Wata

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.