‘Yan kasuwa da jami’ai a yankin kudancin Afirka sun bayyana cewa, ana sa ran manufar soke haraji gaba daya da Sin ta aiwatar kan kayayyakin kasashe 53 na Afirka, za ta samar wa duk fadin nahiyar sabbin damammakin fitar da kayayyakinsu zuwa Sin da zuba jari.
‘Yan kasuwa da jami’an sun bayyana haka ne jiya Alhamis a gun taro ta yanar gizo da sakatariyar kungiyar raya kasashen kudancin Afirka SADC tare da hukumar kasuwanci ta SADC din suka shirya mai taken “Habaka kasuwanci tsakanin kasashen yankin kudancin Afrika da damar zuba jari”, inda mahalarta taron suka tattauna sabbin damammakin kasuwanci da zuba jari da suka bullo a yayin canjin yanayin tattalin arzikin duniya.
Manajan kula da ‘ya’yan itatuwa na kungiyar kasuwancin amfanin gona ta Afirka ta Kudu Wolfe Braude ya bayyana cewa, ya kamata kasashen Afirka su yi amfani da damar shiga cikin babbar kasuwar Sin mai yawan jama’a.
Shugaban hukumar kasuwanci ta kungiyar SADC Kulekani Mathe ya bayyana cewa, ya kamata yankin ya karfafa karfin takara tsakanin masana’antu, da zurfafa tsarin yanki na bai daya, da kuma samar da yanayi mai dorewa ga ci gaban kasuwanci da zuba jari. (Amina Xu)














Discussion about this post