A rana ta biyu ta taron dandalin tattauna batun tafiyar da hakkokin dan Adam na duniya na 2026, wakilai daga kasashen duniya sun bayyana goyon baya ga dabarar Sin ta raya hakkokin dan Adam, inda suka yaba da burinta game da tafiyar da hakkokin dan Adam a duniya.
Cikin jawaban da suka gabatar a jiya Jumma’a, mahalarta da dama sun amince da shawarar Sin ta daukaka batun kare hakkokin dan Adam ta hanyar ci gaba, wadda ita ce ginshikin dabarar Sin a bangaren, kamar yadda Shirin Kasar Sin na Tafiyar da Hakkokin Dan Adam tsakanin shekarar 2021 zuwa 2025, wanda ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar ya wallafa a shekarar 2021, ya bayyana. Karamin ministan kula da raya harkokin iyalai da hakkokin dan Adam na kasar Somaliya, Mohamed Osman Omar, ya nanata cewa, ci gaba ba hanya ce ta bunkasa tattalin arziki kadai ba, tubali ne na mutuncin dan Adam.
Bisa shawarar samar da ci gaba a duniya da Sin ta gabatar, ya kamata al’ummun dukkan kasashe su more hakkokin dan Adam iri daya, ta hanyoyin zamanantar da kai da suka dace da yanayinsu. Wannan na nufin yayin da kasashe ke da buri iri daya na kare hakkokin jama’arsu, kowace na iya bin hanya ta daban da ta dace da yanayinta.
Cikin jawabinta, Maya Sahli-Fadel, shugabar hukumar kare hakkokin dan Adam ta kasar Algeria, ta amince da shawarwarin kasar Sin tare da gabatar da mahanga mai tattare da bangarori da dama game da kare hakkokin dan Adam.
Ta ce dole ne kokarin kare hakkokin dan Adam ya dace da tsarin al’adu da tarihi da tsare-tsaren shari’ar kasa, tare kuma da girmama yanayin kasa da matakan ci gaba da hadin gwiwar kasashe masu tasowa. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post