ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Faru Bayan Harin Sojin Amurka A Nijeriya?

by Sulaiman
5 months ago

Ƙurar da ta taso tun bayan zargin ikirarin kisan gillar Kiristoci a Nijeriya, wanda shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya zargi gwamnatin Nijeriya da yin sakaci ga hare-haren da ake kai wa Kiristoci inda ya yi barazanar dakatar da tallafin Amurka ga Nijeriya da kuma yiwuwar kaddamar da matakin soja don “kawar da” ‘yan ta’adda da ke da alhakin kisan.

 

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da wasu masu faɗa aji a ƙasar, da suka haɗa da shugabannin Siyasa da Malaman Addinin Musulunci, cikin gaggawa suka fara mayar da martani ga shugaban na Amurka kan ikirarin da ya yi.

ADVERTISEMENT
  • Kano Pillars Ta Ƙare Zagayen Farko Na Gasar Firimiyar Nijeriya A Jan Layi
  • Sauya Sheka: Gwamna Abba Ya Yi Daidai

Mai Ba da Shawara na Musamman ga Shugaba Bola Tinubu kan harkokin rashin fahimtar juna, Daniel Bwala, da yake mayar da martani ga wannan zargin na Amurka, Bwala ya ce gwamnatin Tinubu tana jajircewa wajen kare dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da addini ba, yana mai cewa Amurka da Nijeriya sun dade suna hadin gwiwa a yaki da ta’addanci.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

A nasa martanin, Jagoran Siyasa, Tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, bayyana cewa, “Ya kamata a fahimci cewa Nijeriya ƙasa ce mai cikakken ikon kanta. Matsalolin tsaro da muke fuskanta ba su da alaƙa da addini, ƙabila ko ra’ayin siyasa. ‘Yan bindigar da ke addabar mu suna cutar da ‘yan ƙasa ne duka ba tare da bambancewa ba.”

 

Don haka, ya shawarci gwamnatin Amurka da ta daina yin barazana, maimakon haka ta taimaka wa Nijeriya da kayan zamani don magance matsalolin tsaro da ake fama da su.

 

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, shi ma a nasa martanin, ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauki matakin gaggawa kan shugaban Amurka, Donald Trump, bayan barazanar da ya yi na kawo hari Nijeriya.

 

Gumi ya kuma shawarci gwamnatin Tarayya da ta kira Jakadan Amurka domin neman janye wannan barazana, tare da gargaɗin cewa idan hakan bai faru ba, Nijeriya ta yanke hulɗar diflomasiyya da Amurka.

 

Biyo bayan haka ne, tawagar gwamnatin tarayya karkashin jagorancin ofishin mai ba da shawara ga shugaban kasa kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya bazama kasar Amurka, inda ya gana da Sakataren Yaƙin Amurka, Pete Hegseth, a Washington.

 

Duk da kiraye-kiraye da ‘yan Nijeriya suka yi kan tabbatar da cewa, iƙirarin Shugaba Trump kan kisan kiyashi ga Kiristoci a ƙasar ba haka ba ne, kowane ɓangare na ɗanɗana kuɗarsa, amma sai da Amurka ta kawo harin makami mai linzami a wasu yankunan ƙasar.

 

Hare-haren sama da Sojojin Amurka suka kai a Arewa maso Yammacin Nijeriya sun samu martani daga wani ɗan Majalisar Wakilan Amurka, Riley Moore, wanda ya bayyana su a matsayin mataki na farko na kawo ƙarshen kisan jama’a da matsalar tsaro da ta daɗe tana addabar ƙasar.

 

Moore ya ce hare-haren, da aka aiwatar tare da haɗin gwuiwar Gwamnatin Nijeriya, na da nufin dakatar da ayyukan ƙungiyoyin ta’addanci, yana mai cewa Shugaba Donald Trump ya bayyana ƙudurinsa na ganin an kawo ƙarshen kisan Kiristoci a Nijeriya.

 

 

Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya tabbatar da cewa aikin ya gudana ne da goyon bayan Nijeriya, yayin da Ma’aikatar Harkokin Wajen Nijeriya ta ce hare-haren na cikin tsarin haɗin gwuiwar tsaro da ƙasashen waje don yaƙi da ta’addanci.

 

Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa harin saman da Amurka ta kai a ranar Alhamis a Nijeriya an yi su ne da cikakken sani, da goyon baya bayan samun bayanan sirri, da kuma sahalewar Gwamnatin Tarayya.

 

Tuggar ya bayyana haka a ranar Juma’a yayin wata hira da gidan talabijin na Channels, inda ya ce hukumomin Nijeriya sun kasance cikin tattaunawa kai tsaye da Amurka kafin a aiwatar da harin. Ya ce, ya tattauna da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, na tsawon mintuna 19 kafin harin, sannan kuma mintuna biyar kafin a kai harin.

 

Bayan harin saman da rundunar Sojin Amurka ta kai a ranar Kirsimeti a Arewacin Nijeriya, hukumomin soja a Jihar Sokoto sun yi kira ga mazauna jihar da su mika duk wani ragowar bam ko wani baraguzan abubuwan fashewa da suka samu daga wuraren harin.

 

 

Harin saman, wanda aka kai daga daren 25 ga Disamba zuwa safiyar 26 ga Disamba, 2025, ya mayar da hankali ne kan sansanonin ‘yan ta’adda masu alaƙa da ƙungiyar ISWAP a dajin Bauni.

 

 

Duk da tabbacin cewa babu farar hula da suka rasa rayuka, ragowar kayan fashewa da abubuwan da ba a tantance ba da suka faɗo kusa da yankin sun haifar da damuwa kan tsaro. Sojojin sun yi kira ga mazauna yankin da su hanzarta miƙa duk wani ragowar bam ko kayan da suka ɗauka ga hukumomin tsaro don kauce wa fashewar haɗari da kuma taimakawa wajen cikakken bincike na ɓarnar da aka yi.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zan Sauya Sheka In An Bani Tikitin Takarar Shugaban Ƙasa Ko Mataimaki - Kwankwaso 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.