ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

by Dakta Jamil Zarewa
3 years ago
Arfa

Mutane da yawa sun turo da tambayoyi suna son bayanin hukuncin kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta dace da ranar Arfa. Akramakallah a yi mana bayani.

To Dan’uwa Annabi (SAW) ya kwadaitar game da yin Azumi ranar Arfa, inda ya tabbatar da cewa yana kankare zunubin shekaru biyu, Kamar yadda Tirmizi ya rawaito, sai dai ba a son wanda ya je Aikin Hajji ya yi azumin a ranar ARFA, ana so ya shagala da addu’a da zikiri a ranar.

  • Ya Halatta Mu Zubar Da Ciki Ni Da Mijina Idan Likita Ya Gaya Mana Yaron Da Za Mu Haifa Sikila Ne? (Fatawa)

Bukhari da Muslim sun rawaito hadisi daga Annabi (SAW) yana cewa: “Ka da dayanku ya azumci ranar Juma’a ita kadai, sai dai ya hada ta da ranar da take gabaninta ko ranar take kafin ita”.

ADVERTISEMENT

Bisa Hadisin da ya gabata za mu fahimci idan Arafa ta fado ranar Juma’a abin da yake daidai shi ne mutum ya azumci yinin da yake kafin ranar Arfa tare da ranar, saboda ba zai yiwu ya azumci yinin da yake bayan Arfa ba, tun da ya dace da ranar Sallah, Azumi kuma ranar Sallah ya haramta kamar yadda ya zo a Hadisin Umar Dan Khaddab.

Duk da cewa akwai malaman da suka halatta kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta fado ranar Arfa saboda hujjar cewa an hana yin azumi ranar Juma’a ne ita kadai saboda kar a kebance ranar Juma’a da girmamawa.

LABARAI MASU NASABA

Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji

Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani  

Wanda Kuma ya yi azumin Arfa ranar Juma’a, ya yi ne saboda Arfa ba saboda girmama Juma’a ba, sai dai azumin Arfa duk girman falalarsa azumi ne na Nafila, kuma Hadisin da ya hana kebance ranar Juma’a da azumi a kan azumin Nafila yake magana.

Duka kwanaki goman farkon Zulhijja kwanaki ne masu girman falala, babu kwanakin da suka fi su daraja a duniya, idan mutum ya azumci ranar takwas ya hada da ranar Arfa yana kan alkairi Maigirma da kabakin lada mai maiko, sannan zai fita daga sabanin malamai, kuma zai samar da nutsuwa a zuciyarsa.
Allah ne Mafi sani.

Yaya Hukuncin Kame Baki Ranar Idin Babbar Sallah?

Shin akwai wata madogara game da kame baki ranar idin babbar sallah ga wanda zai yi layya?
Wa alaikum assalam, Tabbas Tirmizy ya rawaito a hadisi mai lamba ta:542 cewa: “Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance ba ya cin wani abu ranar idin layya har sai ya dawo daga sallar idi.” Albani ya inganta shi. Sai dai hadisin bai bambance tsakanin wanda ya yi layya ba da wanda bai yi ba. Ban san wani daili ba ga wanda ya ce sai naman layya za a fara ci.
Allah ne mafi sani.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
Dausayin Musulunci

Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji

December 12, 2025
Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani   
Dausayin Musulunci

Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani  

December 5, 2025
Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani
Dausayin Musulunci

Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

November 28, 2025
Next Post
Tsuntsaye Jan-baki

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.