• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

by Dakta Jamil Zarewa
3 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Arfa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutane da yawa sun turo da tambayoyi suna son bayanin hukuncin kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta dace da ranar Arfa. Akramakallah a yi mana bayani.

To Dan’uwa Annabi (SAW) ya kwadaitar game da yin Azumi ranar Arfa, inda ya tabbatar da cewa yana kankare zunubin shekaru biyu, Kamar yadda Tirmizi ya rawaito, sai dai ba a son wanda ya je Aikin Hajji ya yi azumin a ranar ARFA, ana so ya shagala da addu’a da zikiri a ranar.

  • Ya Halatta Mu Zubar Da Ciki Ni Da Mijina Idan Likita Ya Gaya Mana Yaron Da Za Mu Haifa Sikila Ne? (Fatawa)

Bukhari da Muslim sun rawaito hadisi daga Annabi (SAW) yana cewa: “Ka da dayanku ya azumci ranar Juma’a ita kadai, sai dai ya hada ta da ranar da take gabaninta ko ranar take kafin ita”.

Bisa Hadisin da ya gabata za mu fahimci idan Arafa ta fado ranar Juma’a abin da yake daidai shi ne mutum ya azumci yinin da yake kafin ranar Arfa tare da ranar, saboda ba zai yiwu ya azumci yinin da yake bayan Arfa ba, tun da ya dace da ranar Sallah, Azumi kuma ranar Sallah ya haramta kamar yadda ya zo a Hadisin Umar Dan Khaddab.

Duk da cewa akwai malaman da suka halatta kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta fado ranar Arfa saboda hujjar cewa an hana yin azumi ranar Juma’a ne ita kadai saboda kar a kebance ranar Juma’a da girmamawa.

Labarai Masu Nasaba

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

Wanda Kuma ya yi azumin Arfa ranar Juma’a, ya yi ne saboda Arfa ba saboda girmama Juma’a ba, sai dai azumin Arfa duk girman falalarsa azumi ne na Nafila, kuma Hadisin da ya hana kebance ranar Juma’a da azumi a kan azumin Nafila yake magana.

Duka kwanaki goman farkon Zulhijja kwanaki ne masu girman falala, babu kwanakin da suka fi su daraja a duniya, idan mutum ya azumci ranar takwas ya hada da ranar Arfa yana kan alkairi Maigirma da kabakin lada mai maiko, sannan zai fita daga sabanin malamai, kuma zai samar da nutsuwa a zuciyarsa.
Allah ne Mafi sani.

Yaya Hukuncin Kame Baki Ranar Idin Babbar Sallah?

Shin akwai wata madogara game da kame baki ranar idin babbar sallah ga wanda zai yi layya?
Wa alaikum assalam, Tabbas Tirmizy ya rawaito a hadisi mai lamba ta:542 cewa: “Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance ba ya cin wani abu ranar idin layya har sai ya dawo daga sallar idi.” Albani ya inganta shi. Sai dai hadisin bai bambance tsakanin wanda ya yi layya ba da wanda bai yi ba. Ban san wani daili ba ga wanda ya ce sai naman layya za a fara ci.
Allah ne mafi sani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Da Ke Kula Da Gidajen Yarin Nijeriya Na Cigiyar Fursunoni 69 Da Suka Tsere Daga Kuje

Next Post

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

Related

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

3 days ago
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa
Dausayin Musulunci

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

1 week ago
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)

2 weeks ago
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (3)

3 weeks ago
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)

1 month ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

2 months ago
Next Post
Tsuntsaye Jan-baki

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

LABARAI MASU NASABA

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.