• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

by Dakta Jamil Zarewa
3 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Arfa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutane da yawa sun turo da tambayoyi suna son bayanin hukuncin kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta dace da ranar Arfa. Akramakallah a yi mana bayani.

To Dan’uwa Annabi (SAW) ya kwadaitar game da yin Azumi ranar Arfa, inda ya tabbatar da cewa yana kankare zunubin shekaru biyu, Kamar yadda Tirmizi ya rawaito, sai dai ba a son wanda ya je Aikin Hajji ya yi azumin a ranar ARFA, ana so ya shagala da addu’a da zikiri a ranar.

  • Ya Halatta Mu Zubar Da Ciki Ni Da Mijina Idan Likita Ya Gaya Mana Yaron Da Za Mu Haifa Sikila Ne? (Fatawa)

Bukhari da Muslim sun rawaito hadisi daga Annabi (SAW) yana cewa: “Ka da dayanku ya azumci ranar Juma’a ita kadai, sai dai ya hada ta da ranar da take gabaninta ko ranar take kafin ita”.

Bisa Hadisin da ya gabata za mu fahimci idan Arafa ta fado ranar Juma’a abin da yake daidai shi ne mutum ya azumci yinin da yake kafin ranar Arfa tare da ranar, saboda ba zai yiwu ya azumci yinin da yake bayan Arfa ba, tun da ya dace da ranar Sallah, Azumi kuma ranar Sallah ya haramta kamar yadda ya zo a Hadisin Umar Dan Khaddab.

Duk da cewa akwai malaman da suka halatta kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta fado ranar Arfa saboda hujjar cewa an hana yin azumi ranar Juma’a ne ita kadai saboda kar a kebance ranar Juma’a da girmamawa.

Labarai Masu Nasaba

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah

Wanda Kuma ya yi azumin Arfa ranar Juma’a, ya yi ne saboda Arfa ba saboda girmama Juma’a ba, sai dai azumin Arfa duk girman falalarsa azumi ne na Nafila, kuma Hadisin da ya hana kebance ranar Juma’a da azumi a kan azumin Nafila yake magana.

Duka kwanaki goman farkon Zulhijja kwanaki ne masu girman falala, babu kwanakin da suka fi su daraja a duniya, idan mutum ya azumci ranar takwas ya hada da ranar Arfa yana kan alkairi Maigirma da kabakin lada mai maiko, sannan zai fita daga sabanin malamai, kuma zai samar da nutsuwa a zuciyarsa.
Allah ne Mafi sani.

Yaya Hukuncin Kame Baki Ranar Idin Babbar Sallah?

Shin akwai wata madogara game da kame baki ranar idin babbar sallah ga wanda zai yi layya?
Wa alaikum assalam, Tabbas Tirmizy ya rawaito a hadisi mai lamba ta:542 cewa: “Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance ba ya cin wani abu ranar idin layya har sai ya dawo daga sallar idi.” Albani ya inganta shi. Sai dai hadisin bai bambance tsakanin wanda ya yi layya ba da wanda bai yi ba. Ban san wani daili ba ga wanda ya ce sai naman layya za a fara ci.
Allah ne mafi sani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Da Ke Kula Da Gidajen Yarin Nijeriya Na Cigiyar Fursunoni 69 Da Suka Tsere Daga Kuje

Next Post

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

Related

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

2 weeks ago
Kyawawan Abubuwa Da Allah Ya Yi Wa Manzon Allah (SAW) Na Girmamawa
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah

3 weeks ago
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

4 weeks ago
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (6)
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (6)

1 month ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

1 month ago
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa
Dausayin Musulunci

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

2 months ago
Next Post
Tsuntsaye Jan-baki

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.