ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Halatta Mu Zubar Da Ciki Ni Da Mijina Idan Likita Ya Gaya Mana Yaron Da Za Mu Haifa Sikila Ne? (Fatawa)

by Dakta Jamil Zarewa
4 years ago
Ciki

Assalamu alaikum mallam, ni AS ce mijina ma ma haka a ‘genotype’, yarana biyu babban yana da AA karamar ‘AS’ duk sanda na sami ciki muna zuwa a duba mana genotype din babyn da ke cikin, likitoci suka tabbatar da SS ne sai musa a cire amma bai kaiwa ‘4months’ muke cirewa, mallam meye hukuncin yin hakan?

Wa alaikumus salaam wa rahmatullahi wa barakaatuhu. To ‘yar’uwa Malamai sun yi ijma’i a kan haramcin zubar da ciki bayan an busa masa rai, saboda ya zama kashe rai ba da hakki ba.

Amma sun yi sabani game da zubar da ciki kafin ya kai watanni hudu, wasu sun haramta, wasu kuma sun halatta wasu sun karhanta.

ADVERTISEMENT

Amma abin da yake daidai shi ne ya halatta a zubar da cikin da bai kai wata hudu ba, idan akwai lalura, zubar da cikin Sikila ba dole ya zama lalura ba, tun da ana iya haihuwarsa ya rayu, ya bauta wa Allah ya amfani al’uma, don haka barin cikin shi ne ya fi, sai dai idan kuka zubar kafin ya cika wata hudu saboda matsalar da kuke tunanin yaron zai iya fuskanta a rayuwarsa ba za a ce kun yi laifi ba, tun da bai zama mutum ba, kuma ba za a tashe shi ranar alkiyama ba.
Allah ne mafi sani.

Macen Da Ba Ta Haila Saboda Tsarin Iyali, Ya Za Ta Yi Idda Idan Aka Sake Ta?

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Assalamu alaikum. Malam macen da ba ta haila saboda tsarin iyali ‘family planning’ na wasu watanni, yaya za ta yi idan aka sake ta?
Allah ya kara Ikhlasi.
Wa alaikum assalam. Za ta jira har ta ga jini uku, ko da kuwa za ta yi shekaru (30) kamar yadda aya ta (228) a Suratul Bakara ta yi bayani.
Ina yi wa mata nasiha su nisanci yawancin magunguna da alluran tsarin iyali saboda suna sabbba matsaloli.
Duk da cewa tsarin iyali na wucin gadi ya halatta, sai dai imani da cewa: kowanne abin haihuwa da arzikinsa yake zuwa yana da muhimmanci, saboda hakan zai sa kowa ya samu nutsuwa, ya daina tsorata da yawan yaran da zai haifa.
Allah ne mafi sani.

Mijina Ya Sake Ni Da Danyen Goyo, Yaya Iddata?

Assalamu Alaikum, Dr. Tambaya ce: Mace mijinta ya sake ta bayan ta haihu da danyen goyo, ya iddarta za ta kasance? Allah ya kara wa Dr. Ikhlasi.
Wa alaikum assalam. Za ta jira jini uku kamar yadda aya ta (228) a Suratul Bakara ta tabbatar da hakan, ba za ta yi aure ba har sai ta kammala su.
Allah ya kara mana ikhlasi a duka lamuranmu.
Allah ne mafi sani.

Ciki
Dakta Jamil Zarewa
+ postsBio
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Zan Iya Cin Bashin Banki Na Biya Aikin Hajji?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Mene Ne Hukuncin Koyon Ilimin Taurari A Shari’a?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Taskira

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
Taskira

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
Taskira

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Next Post
Brazil Ta Ci Gaba Da Zama Ta Daya A Duniya

Brazil Ta Ci Gaba Da Zama Ta Daya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.