Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya buƙaci jam’iyyun siyasa a Nijeriya su rungumi aƙida domin ƙarfafa dimokuradiyyar ƙasar.
Da yake jawabi a ranar Laraba a Abuja yayin ƙaddamar da littafin “Nigeria’s Journey to Democratic Rule” wanda Onyekachi Eze-Opezulu ya wallafa, Ganduje ya ce rashin ingantacciyar aƙidae siyasa ya raunana tsarin jam’iyyu tare da sa ‘yan siyasa sauya jam’iyya saboda son rai maimakon bin ƙa’idoji.
Ya ce ya kamata jam’iyyun siyasa su kasance da manufofi da tsare-tsare bayyanannu domin al’umma su san abin da kowace jam’iyya ta tsaya a kai.
A cewarsa, inganta dimokuraɗiyya a jam’iyyu da kuma mayar da hankali kan abubuwam da suka shafi ci gaban ƙasa zai kara wa jama’a kwarin gwiwa ga tsarin dimokuradiyya.
Ganduje ya bayyana littafin a matsayin muhimmin abu wajen adana tarihin dimokuraɗiyyar Nijeriya, yana mai cewa zai zama abin amfani ga ɗalibai, masu bincike da shugabannin siyasa wajen fahimtar yadda dimokuraɗiyya ta bunƙasa a ƙasar.
Ya ce dimokuraɗiyya ba ta tsaya ga gudanar da zaɓe kaɗai ba, face tana buƙatar bin doka, cibiyoyi masu ƙarfi, sahihin zaɓe, jam’iyyun siyasa masu inganci da kuma tsaro.
Ya buƙaci shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki su ci gaba da ƙarfafa waɗannan ginshiƙai domin tabbatar da cewa dimokuraɗiyya tana amfanar al’ummar Nijeriya.
Ganduje ya kuma taya marubucin littafin murna, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa littafin zai zama muhimmin jigo ga manazarta da ‘yan baya masu zuwa.













