Sabon Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane, Muttaqha Darma, ya yi alƙawarin amfani da tsarin shugabanci na haɗin gwiwa domin magance matsalar ƙarancin gidaje a Nijeriya da kuma sauƙaƙa samun gidaje masu araha a faɗin ƙasar.
Da yake magana yayin bikin karɓar aiki da aka gudanar a Abuja ranar Litinin, Darma ya ce gwamnatinsa za ta bai wa haɗin kai da masu ruwa da tsaki a ɓangaren muhimmanci domin cimma manufofinta.
Ya ce: “Za mu yi abin da zan kira shugabanci tare da haɗin kai. Ba wai mu jagoranta kaɗai ba ne, dole ne mu nemi haɗin kan sauran waɗanda ke cikin wannan masana’anta. Haka kuma da waɗanda ba sa cikinta kai tsaye amma suna da muhimmanci gare ta.
Za mu kafa ma’aunin tantance aiki.”Ministan ya ƙara da cewa tawagarsa za ta kasance mai ɗaukar alhakin cimma manufofi masu aunuwa, yana mai ƙarfafa masu ruwa da tsaki da su ɗora masa alhakin idan ba a cimma waɗannan manufofi ba.















Discussion about this post