Mazauna ƙauyen Kurawa da ke ƙaramar hukumar Sabon Birni a Jihar Sokoto sun nuna fargaba kan wata cuta da ake zargin sankarau ce, wadda ake cewa ta yi sanadin mutuwar mutane da dama, musamman yara da matasa.
A cewar rahoton Daily Trust, majiyoyi daga cibiyar lafiya ta ƙauyen sun bayyana cewa lamarin ya ƙara tsananta a kwanakin baya-bayan nan, inda ake samun mutuwar mutum biyu zuwa uku a kullum, musamman tsakanin masu shekaru biyu zuwa 20.
Barkewar cutar ta haddasa firgici a yankin, yayin da mutane da yawa ke tururuwar zuwa asibiti domin neman magani kan wata “cuta da ba a san ta ba,” kamar yadda mazauna yankin suka bayyana.
Wani ma’aikacin lafiya da ya nemi a sakaya sunansa ya ce cibiyar lafiyar ta cika maƙil da marasa lafiya.
“Mutane na zuwa asibiti kullum da yawa domin neman magani. Mun cika maƙil kuma ba mu san mene ne ke kashe mutanenmu kusan kullum ba,” in ji shi.
Majiyoyi sun ce da dama daga cikin waɗanda suka mutu sun rasu ne kafin a samu cikakken gano irin cutar da ke damunsu.
Daga baya an shawarci mazauna yankin da su guji kwana a wuraren da babu iska saboda tsananin zafi da ake zargin yana taimakawa wajen yaɗuwar cutar.
Mazauna yankin sun ce alamomin cutar sun haɗa da suma, matsanancin ciwon wuya, amai, gudawa, zazzabi mai tsanani, da kuma fitar kumfa daga baki a wasu lokuta — alamomin da suka yi kama da na cutar sankarau.















Discussion about this post